< Maimaitawar Shari’a 24 >

1 Idan mutum ya auri mata, daga baya ba tă gamshe shi ba domin ya gano wani abu marar kyau game da ita, ya ba ta takardar saki, ya kuma kore ta daga gidansa,
Si un homme a pris une femme, s'il a cohabité avec elle et s'il arrive qu'elle n'ait point trouvé grâce devant lui, parce qu'il aura remarqué en elle quelque difformité; s'il a écrit à son sujet un acte de divorce, s'il le lui a remis, et s'il l'a expulsée de sa maison;
2 in bayan ta bar gidansa ta zama matar wani dabam,
Si, étant partie, elle est devenue la femme d'un autre époux;
3 sai mijinta na biyu ya ƙi ta, ya ba ta takardan saki, ya kore ta daga gidansa, ko kuwa ya mutu,
Si ce dernier époux l'a pareillement prise en haine, lui a écrit aussi un acte de divorce et le lui a remis, et s'il vient à mourir,
4 to, kada mijinta na farko, wanda ya sake ta yă sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Wannan zai zama abin ƙyama a gaban Ubangiji. Kada ku kawo zunubi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
Il ne sera point permis au premier époux qui l'aura congédiée de la reprendre pour femme, après qu'elle aura été souillée; ce serait une abomination devant le Seigneur votre Dieu; gardez-vous de souiller la terre que le Seigneur votre Dieu vous donne pour héritage.
5 In mutum bai daɗe da aure ba, kada a sa yă je yaƙi, ko yă yi wani aiki. Gama zai huta shekara guda a gida, yă faranta wa matar da ya aura rai.
Si un homme a pris femme récemment, il n'ira pas à la guerre, on ne le chargera d'aucune affaire, il restera tranquille à sa maison; pendant un an, il se réjouira de la femme qu'il aura épousée.
6 Kada ku karɓi jinginar dutsen niƙa tare da ɗan dutsen niƙan, domin yin haka zai zama karɓar jinginar rai ne.
Tu ne prendras pas en nantissement les meules du moulin, ni celle de dessous, ni celle de dessus, car les meules sont le nantissement de la vie.
7 Idan aka kama wani yana satar ɗan’uwansa mutumin Isra’ila domin yă sa ya zama bawansa, ko yă sayar da shi, sai a kashe ɓarawon nan. Haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.
Si un homme est convaincu d'avoir volé un de ses frères fils d'Israël, si, après s'être rendu maître de lui, il l'a vendu, il mourra, et tu auras déracine le mal du milieu de vous.
8 Game da cututtukan kuturta, sai ku lura, ku yi yadda firistocin da suke Lawiyawa suka umarce ku. Dole ku lura ku bi abin da na umarce su.
Garde-toi avec soin de la tache de la lèpre; tu veilleras à suivre en toute chose la règle que prescriront les prêtres lévites; tu veilleras à faire ce que je t'ai ordonné.
9 Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Miriyam a hanya, bayan kun fito Masar.
Souviens-toi de ce que le Seigneur ton Dieu a fait à Marie, durant votre voyage au sortir de l'Egypte.
10 Sa’ad da kuka ba da rance na kowane iri ga maƙwabcinku, kada ku shiga gidansa don karɓar wani abu a matsayin jingina.
Si ton prochain est ton débiteur, quelle que soit la dette, tu n'entreras pas en sa maison pour y prendre de lui un gage.
11 Ku tsaya a waje ku bar mutumin da yake karɓan rancen yă kawo muku abin da zai bayar a matsayin jingina.
Tu te tiendras dehors, et l'homme t'apportera son gage.
12 In matalauci ne, kada ku kwana da abin da zai bayar a matsayin jingina a wurinku.
Si l'homme est pauvre, tu ne te remettras pas au lit, ayant son gage.
13 Ku mayar da rigarsa a fāɗuwar rana saboda yă sami abin rufuwa. Yin haka zai sa yă gode muku, za a kuma ɗauka wannan a matsayin aikin adalci da kuka yi a gaban Ubangiji Allahnku.
Tu le lui rendras vers le coucher du soleil; qu'il dorme dans son manteau, et il te bénira, et il attirera sur toi la miséricorde du Seigneur ton Dieu.
14 Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.
Tu ne feras pas tort de son salaire au pauvre ni à l'indigent, soit de tes frères, soit des prosélytes établis en tes villes.
15 Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.
Tu lui paieras son salaire le jour même; que le soleil ne se couche pas sur son salaire; car il est pauvre, il ne trouverait rien chez lui, il crierait contre toi au Seigneur, et tu te serais chargé d'un péché.
16 Ba za a kashe iyaye a maimakon’ya’yansu ba, ba kuwa za a kashe’ya’ya a maimakon iyayensu ba; kowa ya yi zunubi, shi za a kashe.
Les pères ne mourront pas pour leurs enfants, ni les fils pour leurs pères; chacun mourra à cause de son propre péché.
17 Ba za ku danne hakkin baƙon da yake zama a cikinku ko na marayu ba, ba za ku ɗauki rigar matar da mijinta ya mutu a matsayin jingina ba.
Tu ne feras point dévier la justice au sujet de l'étranger, de l'orphelin, de la veuve; tu ne prendras pas en nantissement le vêtement de la veuve.
18 Ku tuna dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuwa ya fisshe daga can. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
Souviens-toi que tu as été esclave en la terre d'Egypte, et que le Seigneur ton Dieu t'en a délivré; c'est pour cela que je te prescris d'observer ces règles.
19 Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
Lorsque tu auras fait la moisson de ton champ, si une javelle a été oubliée dans ton champ, tu n'y retourneras pas pour l'aller prendre; elle sera pour l'étranger, l'orphelin ou la veuve, afin que le Seigneur te bénisse en toutes les œuvres de tes mains.
20 Sa’ad da kuka kakkaɓe’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
Lorsque tu auras fait la récolte de tes olives, tu ne retourneras pas glaner celles que tu aurais oubliées; elles seront pour l'étranger, l'orphelin ou la veuve; souviens-toi que tu as été esclave en la terre d'Egypte et que le Seigneur ton Dieu t'en a délivré; c'est pour cela que je te prescris d'observer ces règles.
21 Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
Lorsque tu auras vendangé ta vigne, tu ne vendangeras pas derechef pour prendre les grappes que tu aurais oubliées; elles seront pour l'étranger, l'orphelin ou la veuve.
22 Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
Souviens-toi que tu as été esclave en la terre d'Egypte, et que le Seigneur ton Dieu t'en a délivré; c'est pour cela que je te prescris ces règles.

< Maimaitawar Shari’a 24 >