< Maimaitawar Shari’a 24 >
1 Idan mutum ya auri mata, daga baya ba tă gamshe shi ba domin ya gano wani abu marar kyau game da ita, ya ba ta takardar saki, ya kuma kore ta daga gidansa,
“Suppose a man marries a woman and later decides that he does not want her because there is something about her that he doesn’t like. And suppose he writes on paper that he is divorcing her, and he gives the paper to her [SYN] and sends her away from his house.
2 in bayan ta bar gidansa ta zama matar wani dabam,
Then suppose that she goes and marries another man,
3 sai mijinta na biyu ya ƙi ta, ya ba ta takardan saki, ya kore ta daga gidansa, ko kuwa ya mutu,
and that man [later also] decides that he does not like her, and he also writes on paper that he is divorcing her, and he sends her away from his house. Or, suppose that the second husband dies.
4 to, kada mijinta na farko, wanda ya sake ta yă sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Wannan zai zama abin ƙyama a gaban Ubangiji. Kada ku kawo zunubi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
If either of those things happens, her first husband must not marry her again. He must consider that she has become unacceptable to Yahweh. Yahweh would consider it to be disgusting [if he married her again]. You must not sin [MTY] by doing that in the land that Yahweh our God is giving to you.”
5 In mutum bai daɗe da aure ba, kada a sa yă je yaƙi, ko yă yi wani aiki. Gama zai huta shekara guda a gida, yă faranta wa matar da ya aura rai.
“When some man has recently become married, he must not [be required to] become a soldier in the army or be required to do any other work [for the government] for one year [after being married]. He should stay happily at home with his wife for that year.
6 Kada ku karɓi jinginar dutsen niƙa tare da ɗan dutsen niƙan, domin yin haka zai zama karɓar jinginar rai ne.
“Anyone who lends money to someone else [is allowed to require that person to give him something] to guarantee [that he will pay back the money that he borrowed. But] he must not take from him his (millstone/stone for grinding grain). That would be taking [the millstone that his family needs to grind the grain to make the bread] they need to stay alive.
7 Idan aka kama wani yana satar ɗan’uwansa mutumin Isra’ila domin yă sa ya zama bawansa, ko yă sayar da shi, sai a kashe ɓarawon nan. Haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.
“If someone kidnaps/steals a fellow Israeli to cause that person to become his slave or to sell him [to become someone else’s slave], you must execute the person who did that. By doing that, you will get rid of this evil among you.
8 Game da cututtukan kuturta, sai ku lura, ku yi yadda firistocin da suke Lawiyawa suka umarce ku. Dole ku lura ku bi abin da na umarce su.
“If you are suffering from (leprosy/a dreaded skin disease), be sure to do everything that the priests, who are from the tribe of Levi, tell you to do. Obey carefully the instructions that I have given to them.
9 Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Miriyam a hanya, bayan kun fito Masar.
Do not forget what Yahweh our God did to Miriam, [when she became a leper], after your ancestors left Egypt.
10 Sa’ad da kuka ba da rance na kowane iri ga maƙwabcinku, kada ku shiga gidansa don karɓar wani abu a matsayin jingina.
“When you lend something to someone, do not go into his house to take the cloak that he says that he will give you to guarantee [that he will return what he has borrowed].
11 Ku tsaya a waje ku bar mutumin da yake karɓan rancen yă kawo muku abin da zai bayar a matsayin jingina.
Stand outside his house, and the man to whom you are lending something will bring the cloak out to you.
12 In matalauci ne, kada ku kwana da abin da zai bayar a matsayin jingina a wurinku.
But if he is poor, do not keep that cloak all night.
13 Ku mayar da rigarsa a fāɗuwar rana saboda yă sami abin rufuwa. Yin haka zai sa yă gode muku, za a kuma ɗauka wannan a matsayin aikin adalci da kuka yi a gaban Ubangiji Allahnku.
When the sun sets, take the cloak back to him, in order that he may wear it while he sleeps. If you do that, he will [ask God to] bless you, and Yahweh our God will be pleased with you.
14 Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.
“Do not mistreat any servants whom you have hired who are poor and needy [DOU], whether they are Israelis or foreigners who are living in your town.
15 Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.
Every day, before sunset, you must pay/give them the money that they have earned. They are poor and they need to get their pay. If you do not pay them right away, they will cry out against you to Yahweh, and he will punish [MTY] you for having sinned like that.
16 Ba za a kashe iyaye a maimakon’ya’yansu ba, ba kuwa za a kashe’ya’ya a maimakon iyayensu ba; kowa ya yi zunubi, shi za a kashe.
“Parents must not be executed for crimes that their children have committed, and children must not be executed for crimes that their parents have committed. People should be executed only for the crimes that they themselves have committed.
17 Ba za ku danne hakkin baƙon da yake zama a cikinku ko na marayu ba, ba za ku ɗauki rigar matar da mijinta ya mutu a matsayin jingina ba.
“You must [LIT] do for foreigners [who live] among you and for orphans what the laws state must be done for them. And [if you lend something to] a widow, do not take her coat from her as a guarantee [that she will return it].
18 Ku tuna dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuwa ya fisshe daga can. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
Do not forget that [you had great hardships/troubles when] you were slaves in Egypt, and Yahweh our God rescued you from there. That is why I am commanding you [to help others who have troubles].
19 Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
“When you harvest your crops, if you have forgotten [that you left] one bundle in the field, do not go back to get it. [Leave it there] for foreigners, orphans, and widows. If you do that, Yahweh will bless you in everything that you do.
20 Sa’ad da kuka kakkaɓe’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
And when you have harvested/picked all your olives from the trees once, do not go back [to pick the ones that are still] on the trees.
21 Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
[Similarly], when you pick the grapes in your vineyard, do not go back a second time [to try to find more]. Leave them for the foreigners, orphans, and widows [among you].
22 Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
Do not forget that [Yahweh was kind to you when] you were slaves in Egypt. That is why I am commanding you [to be kind to those who are needy].”