< Maimaitawar Shari’a 23 >

1 Duk wanda aka daƙe, ko yanke gabansa, ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.
He that is wounded, or cut off in his secrets, shall not enter into the congregation of the LORD.
2 Duk wanda aka haifa ta wurin cikin shege, har tsara ta goma, zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba, har zuwa tsara ta goma.
A bastard shall not enter into the congregation of the LORD; even to his tenth generation shall he not enter into the congregation of the LORD.
3 Ba mutumin Ammon, ko mutumin Mowab, ko kuwa wani zuriyarsu da zai shiga taron jama’ar Ubangiji, har tsara ta goma.
An Ammonite or Moabite shall not enter into the congregation of the LORD; even to their tenth generation shall they not enter into the congregation of the LORD for ever:
4 Gama ba su zo sun tarye ku da burodi da ruwa a hanyarku, sa’ad da kuka fito daga Masar ba, sai ma suka yi haya Bala’am ɗan Beyor daga Fetor a Aram-Naharayim yă furta la’ana a kanku.
Because they met you not with bread and with water in the way, when ye came forth from Egypt; and because they hired against thee Balaam the son of Beor of Pethor of Mesopotamia, to curse thee.
5 Amma Ubangiji Allahnku bai saurari Bala’am ba, sai ya mai da la’anar ta koma albarka gare ku, domin Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
Nevertheless the LORD thy God would not hearken to Balaam; but the LORD thy God turned the curse into a blessing to thee, because the LORD thy God loved thee.
6 Kada ku yi yarjejjeniyar abuta da su, muddin kuna da rai.
Thou shalt not seek their peace nor their prosperity all thy days for ever.
7 Kada ku yi ƙyamar mutumin Edom, gama mutumin Edom ɗan’uwanku ne. Kada ku yi ƙyamar mutumin Masar, domin kun yi zama baƙunta a ƙasarsa.
Thou shalt not abhor an Edomite; for he is thy brother: thou shalt not abhor an Egyptian; because thou wast a stranger in his land.
8 ’Ya’yan da aka haifa musu na tsara ta uku za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.
The children that are begotten by them shall enter into the congregation of the LORD in their third generation.
9 Sa’ad da kuka yi sansani don ku yi yaƙi da abokan gābanku, ku kiyaye kanku daga duk wani abu marar tsabta.
When the host goeth forth against thy enemies, then keep thee from every wicked thing.
10 In ɗaya daga cikin mazanku ya ƙazantu saboda zubar da maniyyi, sai yă fita daga sansani yă zauna waje da sansani.
If there shall be among you any man, that is not clean by reason of uncleanness that chanceth to him by night, then shall he go abroad out of the camp, he shall not come within the camp:
11 Amma yayinda yamma ke gabatowa sai yă wanke kansa, da fāɗuwar rana kuwa sai yă koma cikin sansani.
But it shall be, when evening cometh on, he shall wash himself with water: and when the sun is down, he shall come into the camp again.
12 Ku keɓe wuri waje da sansani inda za ku iya zuwa don yin bayan gari.
Thou shalt have a place also outside the camp, where thou shalt go forth abroad:
13 Sai ku ɗauki wani abin tona ƙasa, sa’ad da kuka yi bayan gari, sai ku tona rami, ku rufe bayan garinku.
And thou shalt have a shovel among thy weapons; and it shall be, when thou wilt ease thyself abroad, thou shalt dig with it, and shalt turn back and cover that which cometh from thee:
14 Gama Ubangiji Allahnku yana zagawa a cikin sansaninku don yă tsare ku, yă kuma bashe abokan gābanku gare ku. Dole sansaninku yă kasance da tsarki, saboda kada yă ga wani abu marar kyau a cikinku, har yă juya daga gare ku.
For the LORD thy God walketh in the midst of thy camp, to deliver thee, and to give up thy enemies before thee; therefore shall thy camp be holy: that he may see no unclean thing in thee, and turn away from thee.
15 In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
Thou shalt not deliver to his master the servant who hath escaped from his master to thee:
16 Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
He shall dwell with thee, even among you, in that place which he shall choose in one of thy gates, where it pleaseth him best: thou shalt not oppress him.
17 Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
There shall be no harlot of the daughters of Israel, nor a sodomite of the sons of Israel.
18 Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
Thou shalt not bring the hire of an harlot, or the price of a dog, into the house of the LORD thy God for any vow: for even both these are abomination to the LORD thy God.
19 Kada ku nemi ɗan’uwanku yă biya bashin da kuka ba shi da ruwa, ko kuɗi, ko abinci, ko kowane irin abin da yana iya ba da ruwa.
Thou shalt not lend upon interest to thy brother; interest of money, interest of food, interest of any thing that is lent upon interest:
20 Za ku iya nemi ruwa a bashin da kuka ba baƙo, amma ba ɗan’uwanku mutumin Isra’ila ba, domin Ubangiji Allahnku yă sa muku albarka a kowane abin da kuka sa hannunku a kai, a ƙasar da kuke shiga ku ci gādonta.
To a stranger thou mayest lend upon interest; but to thy brother thou shalt not lend upon interest: that the LORD thy God may bless thee in all that thou settest thy hand to in the land where thou goest to possess it.
21 In fa kuka yi alkawari ga Ubangiji Allahnku, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama tabbatacce Ubangiji Allahnku zai neme shi daga gare ku, za ku kuma zama masu laifin zunubi.
When thou shalt vow a vow to the LORD thy God, thou shalt not defer to pay it: for the LORD thy God will surely require it of thee; and it would be sin in thee.
22 Amma in ba ku yi alkawari ba, ba kuwa zai zama muku zunubi ba.
But if thou shalt forbear to vow, it shall be no sin in thee.
23 Duk abin da ya fita daga bakinku, sai ku lura ku cika shi, kamar yadda kuka yarda da kanku, kuka yi alkawarin ga Ubangiji Allahnku da bakinku.
That which is uttered by thy lips thou shalt keep and perform; even a freewill offering, according as thou hast vowed to the LORD thy God, which thou hast promised with thy mouth.
24 In kun shiga gonar inabin maƙwabcinku, za ku iya cin inabin da kuke so, amma kada ku sa wani a kwandonku.
When thou comest into thy neighbour’s vineyard, then thou mayest satisfy thy appetite with grapes at thy own pleasure; but thou shalt not put any in thy vessel.
25 In kun shiga gonar hatsin maƙwabcinku, za ku iya murmure tsabar da hannuwanku, amma kada ku sa lauje ku yanka hatsinsa da yake tsaye.
When thou comest into the standing grain of thy neighbour, then thou mayest pluck the heads with thy hand; but thou shalt not move a sickle to thy neighbour’s standing grain.

< Maimaitawar Shari’a 23 >