< Maimaitawar Shari’a 23 >

1 Duk wanda aka daƙe, ko yanke gabansa, ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.
“Any man whose testicles are crushed or whose penis is cut off shall not be (included as one of/allowed to worship with) Yahweh’s people.
2 Duk wanda aka haifa ta wurin cikin shege, har tsara ta goma, zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba, har zuwa tsara ta goma.
“No (illegitimate person/person whose mother and father were not married), or descendant of that person, extending to the tenth generation, shall be included as one of Yahweh’s people.
3 Ba mutumin Ammon, ko mutumin Mowab, ko kuwa wani zuriyarsu da zai shiga taron jama’ar Ubangiji, har tsara ta goma.
“No one from the Ammon or Moab people-groups shall be (included as one of/allowed to worship with) Yahweh’s people, extending to the tenth generation.
4 Gama ba su zo sun tarye ku da burodi da ruwa a hanyarku, sa’ad da kuka fito daga Masar ba, sai ma suka yi haya Bala’am ɗan Beyor daga Fetor a Aram-Naharayim yă furta la’ana a kanku.
One reason is that their [leaders] refused to give your ancestors food and water when they were traveling from Egypt [to Canaan]. Another reason is that they wanted to pay Balaam, the son of Beor from Pethor [town] in Mesopotamia, to curse you Israelis.
5 Amma Ubangiji Allahnku bai saurari Bala’am ba, sai ya mai da la’anar ta koma albarka gare ku, domin Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
But Yahweh our God did not pay attention to Balaam; instead, he caused Balaam to bless your ancestors, because Yahweh loved them.
6 Kada ku yi yarjejjeniyar abuta da su, muddin kuna da rai.
As long as Israel is a nation, you must not do anything to cause things to go well for those two people-groups or enable them to prosper.
7 Kada ku yi ƙyamar mutumin Edom, gama mutumin Edom ɗan’uwanku ne. Kada ku yi ƙyamar mutumin Masar, domin kun yi zama baƙunta a ƙasarsa.
“But do not despise anyone from the Edom people-group, because they are [descendants of your ancestor Jacob], just like you are. And do not despise people from Egypt, because [they treated your ancestors well when] they first lived in Egypt.
8 ’Ya’yan da aka haifa musu na tsara ta uku za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.
The children and grandchildren of people from Edom and Egypt [who live among you] may be (included among/allowed to worship with) Yahweh’s people.”
9 Sa’ad da kuka yi sansani don ku yi yaƙi da abokan gābanku, ku kiyaye kanku daga duk wani abu marar tsabta.
“When your soldiers are living in tents at a time of fighting your enemies, they must avoid doing things that would make them unacceptable to God.
10 In ɗaya daga cikin mazanku ya ƙazantu saboda zubar da maniyyi, sai yă fita daga sansani yă zauna waje da sansani.
If any soldier becomes unacceptable to God because semen comes out of his body during the night, [the next morning] he must go outside the camp and stay there during that day.
11 Amma yayinda yamma ke gabatowa sai yă wanke kansa, da fāɗuwar rana kuwa sai yă koma cikin sansani.
But in the evening of that day, he must bathe himself, and at sunset he is allowed to come back into the camp.
12 Ku keɓe wuri waje da sansani inda za ku iya zuwa don yin bayan gari.
“Your soldiers must have a toilet area outside the camp where you can go [when you need to].
13 Sai ku ɗauki wani abin tona ƙasa, sa’ad da kuka yi bayan gari, sai ku tona rami, ku rufe bayan garinku.
[When you go to fight against your enemies], carry a stick along with your weapons, in order that when you need to defecate [EUP], you can dig a hole with the stick, and then cover up the hole [when you have finished defecating].
14 Gama Ubangiji Allahnku yana zagawa a cikin sansaninku don yă tsare ku, yă kuma bashe abokan gābanku gare ku. Dole sansaninku yă kasance da tsarki, saboda kada yă ga wani abu marar kyau a cikinku, har yă juya daga gare ku.
You must keep the camp acceptable to Yahweh our God, because he is with you in your camp to protect you and to enable you to defeat your enemies. Do not do anything disgraceful/indecent that would cause Yahweh to abandon you.”
15 In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
“If slaves who escape from their masters come to you [and request you to protect them], do not send them back to their masters.
16 Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
Allow them to stay/live among you, in whatever town they choose, and do not mistreat them.
17 Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
“Do not [allow] any Israeli man or woman [to] become a prostitute at the temple.
18 Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
Also, do not allow any people who earned money from being a prostitute to bring any of that money into the temple of Yahweh our God, even if they solemnly promised to pay that money to Yahweh. Yahweh hates those who are prostitutes.
19 Kada ku nemi ɗan’uwanku yă biya bashin da kuka ba shi da ruwa, ko kuɗi, ko abinci, ko kowane irin abin da yana iya ba da ruwa.
“When you lend money or food or anything else to a fellow Israeli, do not charge them interest.
20 Za ku iya nemi ruwa a bashin da kuka ba baƙo, amma ba ɗan’uwanku mutumin Isra’ila ba, domin Ubangiji Allahnku yă sa muku albarka a kowane abin da kuka sa hannunku a kai, a ƙasar da kuke shiga ku ci gādonta.
You are allowed to charge interest when you lend money to foreigners [who live in your land], but not when you lend money to Israelis. Do this in order that Yahweh our God will bless you in everything that you do in the land that you are about to enter and occupy.
21 In fa kuka yi alkawari ga Ubangiji Allahnku, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama tabbatacce Ubangiji Allahnku zai neme shi daga gare ku, za ku kuma zama masu laifin zunubi.
“When you vow to give something to Yahweh your God [or to do something for him], do it as soon as you can. Yahweh expects you to do what you promised, and if you do not do it, you will be committing a sin.
22 Amma in ba ku yi alkawari ba, ba kuwa zai zama muku zunubi ba.
But if you [SYN] do not vow [to do something], that is not sinful.
23 Duk abin da ya fita daga bakinku, sai ku lura ku cika shi, kamar yadda kuka yarda da kanku, kuka yi alkawarin ga Ubangiji Allahnku da bakinku.
But if you voluntarily promise to do something, you must do it.
24 In kun shiga gonar inabin maƙwabcinku, za ku iya cin inabin da kuke so, amma kada ku sa wani a kwandonku.
“When you walk through someone else’s vineyard, you are allowed to [pick and] eat as many grapes as you want, but you must not [cut some from a vine and carry them away] in a container.
25 In kun shiga gonar hatsin maƙwabcinku, za ku iya murmure tsabar da hannuwanku, amma kada ku sa lauje ku yanka hatsinsa da yake tsaye.
When you walk [along a path] in someone else’s field of grain, you are allowed to pluck/pick some of the grain and eat it, but you must not cut any grain with a sickle [and take it with you].”

< Maimaitawar Shari’a 23 >