< Maimaitawar Shari’a 22 >

1 In kun ga saniya ko tunkiyar ɗan’uwanku wadda ta ɓace, kada ku ƙyale ta, amma ku tabbata kun komar da ita gare shi.
اگر گاو یا گوسفند کسی را سرگردان دیدید، وانمود نکنید که آن را ندیده‌اید، بلکه حتماً آن را به نزد صاحبش برگردانید.
2 In ɗan’uwan ba ya zama kusa da ku, ko kuwa ba ku san shi ba, sai ku kai ta gida ku ajiye ta sai ya zo nemanta. Sa’an nan ku ba shi ita.
اگر صاحبش نزدیک شما زندگی نمی‌کند و یا او را نمی‌شناسید، آن را به مزرعهٔ خود ببرید و در آنجا نگه دارید تا زمانی که صاحبش به دنبال آن بیاید. آنگاه آن را به صاحبش بدهید.
3 Ku yi haka in kun sami jakin ɗan’uwanku, ko rigarsa, ko kowane abin da ya ɓace. Kada ku ƙyale shi.
این قانون شامل الاغ، لباس یا هر چیز دیگری که پیدا می‌کنید نیز می‌شود. نسبت به آن بی‌اعتنا نباشید.
4 In kuka ga jakin ɗan’uwanku, ko saniyarsa ya fāɗi a kan hanya, kada ku ƙyale shi. Ku taimaka, ku tā da shi.
اگر کسی را دیدید که سعی می‌کند گاو یا الاغی را که زیر بار خوابیده است روی پاهایش بلند کند، رویتان را برنگردانید، بلکه به کمکش بشتابید.
5 Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata, gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yin haka.
زن نباید لباس مردانه بپوشد و مرد نباید لباس زنانه به تن کند. این کار در نظر خداوند، خدایتان نفرت‌انگیز است.
6 In kuka ga gidan tsuntsu kusa da hanya, ko a kan itace, ko kuma a ƙasa, mahaifiyar tsuntsun kuwa tana kwance a kan’ya’yanta, ko kuwa a kan ƙwanta, kada ku kama mahaifiyar duk da’ya’yan.
اگر آشیانهٔ پرنده‌ای را روی زمین افتاده ببینید و یا آشیانه‌ای را روی درختی ببینید که پرنده با جوجه‌ها یا تخمهایش در داخل آن نشسته است، مادر و جوجه‌هایش را با هم برندارید؛
7 Za ku iya kwashe’ya’yan, amma ku tabbata kun bar mahaifiyar tă tafi. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai.
مادر را رها کنید برود و فقط جوجه‌هایش را بردارید. اگر چنین کنید زندگی‌تان پربرکت و طولانی خواهد بود.
8 Sa’ad da kuka gina sabon gida, ku ja masa dakali kewaye da rufinku don kada ku jawo laifin zub da jini a kan gidanku in wani ya fāɗi daga kan rufin.
وقتی خانهٔ تازه‌ای می‌سازید، باید دیوار کوتاهی دور تا دور پشت بام بکشید تا از افتادن اشخاص جلوگیری کرده، مسئول مرگ کسی نشوید.
9 Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku; in kuka yi haka, ba abin da kuka shuka ne kaɗai zai ƙazantu ba, amma har da inabinku ma.
در تاکستان خود بذر دیگری نکارید. اگر کاشتید، هم محصول بذر کاشته شده و هم انگورها تلف خواهند شد.
10 Kada ku haɗa bijimi da jaki su yi noma tare.
با گاو و الاغی که به هم یراق شده‌اند شخم نکنید.
11 Kada ku sa rigar ulu da aka gauraye da lilin aka saƙa.
لباسی را که از دو نوع نخ، مثلاً پشم و کتان بافته شده است نپوشید.
12 Ku yi tuntu a kusurwan huɗu na rigar da kuke sa.
در چهار گوشهٔ ردای خود باید منگوله بدوزید.
13 In mutum ya auri mace, bayan ya kwana da ita, sa’an nan ya ƙi ta
اگر مردی با دختری ازدواج کند و پس از همبستر شدن با او، وی را متهم کند که قبل از ازدواج با مرد دیگری روابط جنسی داشته است و بگوید: «وقتی با او ازدواج کردم باکره نبود.»
14 ya kuma zarge ta, ya ba ta mummunan suna, yana cewa, “Na auri wannan mata, amma sa’ad da na kusace ta, ban sami tabbaci cewa ita budurwa ba ce,”
15 sai mahaifin yarinyar da mahaifiyarta su kawo shaida cewa ita budurwa ce wa dattawan gari a ƙofar garin.
آنگاه پدر و مادر دختر باید مدرک بکارت او را نزد مشایخ به دروازۀ شهر بیاورند.
16 Mahaifin yarinyar zai ce wa dattawa, “Na ba da’yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.
پدرش باید به آنها بگوید: «من دخترم را به این مرد دادم تا همسر او باشد، ولی این مرد او را نمی‌خواهد
17 Yanzu ya zage ta cewa, ‘Ban sami’yarku budurwa ba.’ Amma ga shaidar budurcin’yata.” Sa’an nan iyayenta za su shimfiɗa zanen a gaban dattawan garin,
و به او تهمت زده، ادعا می‌کند که دخترم هنگام ازدواج باکره نبوده است. اما این مدرک ثابت می‌کند که او باکره بوده است.» سپس باید پارچه را جلوی مشایخ پهن کنند. مشایخ باید آن مرد را شلّاق بزنند
18 dattawan kuwa za su ɗauki mutumin su hukunta shi.
19 Za su ci masa tara shekel azurfa ɗari, su ba mahaifin yarinyar, domin wannan mutum ya ba wa budurwa mutuniyar Isra’ila mummunan suna. Za tă ci gaba da zama matarsa; ba kuwa zai sake ta ba muddin ransa.
و محکوم به پرداخت جریمه‌ای معادل صد مثقال نقره بکنند، چون به دروغ، یک باکرهٔ اسرائیلی را متهم کرده است. این جریمه باید به پدر دختر پرداخت شود. آن زن، همسر وی باقی خواهد ماند و مرد هرگز نباید او را طلاق بدهد.
20 Amma fa in zarge gaskiya ne, ba a kuwa sami shaidar budurcin yarinyar ba,
ولی اگر اتهامات مرد حقیقت داشته و آن زن هنگام ازدواج باکره نبوده است،
21 sai a kawo ta a ƙofar gidan mahaifinta, a can mazan gari za su jajjefe ta da dutse har tă mutu. Ta yi abin kunya a Isra’ila ta wurin lalaci a yayinda take a gidan mahaifinta. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
مشایخ، دختر را به در خانهٔ پدرش ببرند و مردان شهر او را سنگسار کنند تا بمیرد، چون او در اسرائیل عمل قبیحی انجام داده است و در زمانی که در خانهٔ پدرش زندگی می‌کرده، زنا کرده است. چنین شرارتی باید از میان شما پاک گردد.
22 In aka kama wani yana kwance da matar wani, dole a kashe dukansu biyu, wato, mutumin da ya kwana da matar da kuma matar. Dole a fid da mugu daga Isra’ila.
اگر مردی در حال ارتکاب زنا با زن شوهرداری دیده شود، هم آن مرد و هم آن زن باید کشته شوند. به این ترتیب، شرارت از اسرائیل پاک خواهد شد.
23 In mutum ya sadu da budurwa a gari wadda aka yi alkawarin aure, ya kuma kwana da ita
اگر مردی در شهری دختری را که نامزد دارد ببیند و با او همبستر شود
24 sai ku ɗauki su biyu zuwa ƙofar wannan gari, ku jajjefe su da dutse har su mutum, za a kashe yarinyar domin tana a cikin gari ba ta kuwa yi ihu neman taimako ba, za a kashe mutumin domin ya yi lalata da matar wani. Dole ku fi da mugu daga cikinku.
باید هم دختر و هم مرد را از دروازهٔ شهر بیرون برده، سنگسار کنند تا بمیرند. دختر را به سبب اینکه فریاد نزده و کمک نخواسته است و مرد را به جهت اینکه نامزد مرد دیگری را بی‌حرمت کرده است. چنین شرارتی باید از میان شما پاک شود.
25 Amma in a bayan gari ne mutumin ya sadu da yarinyar da aka yi alkawari aure, ya kuma yi mata fyaɗe, mutumin da ya yi wannan ne kaɗai zai mutu.
ولی اگر چنین عملی خارج از شهر اتفاق بیفتد تنها مرد باید کشته شود، چون دختر گناهی که مستحق مرگ باشد مرتکب نشده است. این، مثل آن است که کسی بر شخصی حمله‌ور شده او را بکشد، زیرا دختر فریاد زده و چون در خارج از شهر بوده، کسی به کمکش نرفته است تا او را نجات دهد.
26 Kada ku yi wa yarinyar kome, ba tă yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Wannan batu ya yi kamar da na mutumin da ya fāɗa wa maƙwabcinsa ya kuma kashe shi.
27 Tun da ya same ta a jeji ne, wataƙila yarinyar ta yi kukan neman taimako, amma babu wani da zai cece ta.
28 In mutum ya sadu da yarinyar da ba a yi alkawarin aurenta ba, ya kuma yi mata fyaɗe, aka kuma kama su,
اگر مردی به دختری که نامزد نشده است تجاوز کند و در حین عمل غافلگیر شود، باید به پدر دختر پنجاه مثقال نقره بپردازد و با آن دختر ازدواج کند و هرگز نمی‌تواند او را طلاق بدهد.
29 sai yă biya mahaifin yarinyar shekel hamsin na azurfa. Dole yă auri yarinyar, gama ya yi lalata da ita. Ba zai taɓa sake ta ba muddin ransa.
30 Kada mutum yă auri matar mahaifinsa, kada yă ƙasƙantar gādon mahaifinsa.
هیچ‌کس نباید زن پدر خود را به زنی گرفته، به پدر خود بی‌حرمتی روا دارد.

< Maimaitawar Shari’a 22 >