< Maimaitawar Shari’a 22 >

1 In kun ga saniya ko tunkiyar ɗan’uwanku wadda ta ɓace, kada ku ƙyale ta, amma ku tabbata kun komar da ita gare shi.
Thou shalt not see thy brother's ox or his lamb go astray, and withdraw thyself from them: thou shalt surely bring them back again unto thy brother.
2 In ɗan’uwan ba ya zama kusa da ku, ko kuwa ba ku san shi ba, sai ku kai ta gida ku ajiye ta sai ya zo nemanta. Sa’an nan ku ba shi ita.
But if thy brother be not nigh unto thee, or thou know him not: then shalt thou take it unto thy own house, and it shall remain with thee until thy brother inquire after it, and then shalt thou restore it to him.
3 Ku yi haka in kun sami jakin ɗan’uwanku, ko rigarsa, ko kowane abin da ya ɓace. Kada ku ƙyale shi.
In like manner shalt thou do with his ass; and in like manner shalt thou do with his raiment; and in like manner shalt thou do with every lost thing of thy brother's, which may have been lost to him, and which thou hast found; thou art not at liberty to withdraw thyself.
4 In kuka ga jakin ɗan’uwanku, ko saniyarsa ya fāɗi a kan hanya, kada ku ƙyale shi. Ku taimaka, ku tā da shi.
Thou shalt not see thy brother's ass or his ox fallen down by the way, and withdraw thyself from them: thou shalt surely help him to lift them up again.
5 Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata, gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yin haka.
A woman shall not have upon her the apparel of a man, and a man shall not put on a woman's garment; for an abomination unto the Lord thy God are all who do this.
6 In kuka ga gidan tsuntsu kusa da hanya, ko a kan itace, ko kuma a ƙasa, mahaifiyar tsuntsun kuwa tana kwance a kan’ya’yanta, ko kuwa a kan ƙwanta, kada ku kama mahaifiyar duk da’ya’yan.
If a bird's nest chance to be before thee in the way, on any tree, or on the ground, with young ones, or with eggs, and the mother be sitting upon the young, or upon the eggs: thou shalt not take the mother with the young;
7 Za ku iya kwashe’ya’yan, amma ku tabbata kun bar mahaifiyar tă tafi. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai.
But thou shalt surely let the mother go, and the young thou mayest take to thyself; in order that it may be well with thee, and that thou mayest live many days.
8 Sa’ad da kuka gina sabon gida, ku ja masa dakali kewaye da rufinku don kada ku jawo laifin zub da jini a kan gidanku in wani ya fāɗi daga kan rufin.
When thou buildest a new house, thou shalt make a battlement for thy roof; that thou bring not blood upon thy house, if any one were to fall from there.
9 Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku; in kuka yi haka, ba abin da kuka shuka ne kaɗai zai ƙazantu ba, amma har da inabinku ma.
Thou shalt not sow thy vineyard with divers seeds; that the ripe fruit of thy seed which thou hast sown, and the fruit of the vineyard, be not defiled.
10 Kada ku haɗa bijimi da jaki su yi noma tare.
Thou shalt not plough with an ox and an ass together.
11 Kada ku sa rigar ulu da aka gauraye da lilin aka saƙa.
Thou shalt not wear a garment of divers sorts, of woolen and linen together.
12 Ku yi tuntu a kusurwan huɗu na rigar da kuke sa.
Thou shalt make thyself fringes upon the four corners of thy vesture, wherewith thou coverest thyself.
13 In mutum ya auri mace, bayan ya kwana da ita, sa’an nan ya ƙi ta
If any man take a wife, and go in unto her, and hate her,
14 ya kuma zarge ta, ya ba ta mummunan suna, yana cewa, “Na auri wannan mata, amma sa’ad da na kusace ta, ban sami tabbaci cewa ita budurwa ba ce,”
And he lay an accusation against her, and spread abroad an evil name upon her, and say, This woman I took [for wife], and when I came near to her, I found no tokens of virginity in her:
15 sai mahaifin yarinyar da mahaifiyarta su kawo shaida cewa ita budurwa ce wa dattawan gari a ƙofar garin.
Then shall the father of the damsel, and her mother, take and bring forth the tokens of the damsel's virginity unto the elders of the city, to the gate.
16 Mahaifin yarinyar zai ce wa dattawa, “Na ba da’yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.
And the father of the damsel shall say unto the elders, My daughter I gave unto this man for wife; but he hath conceived hatred toward her;
17 Yanzu ya zage ta cewa, ‘Ban sami’yarku budurwa ba.’ Amma ga shaidar budurcin’yata.” Sa’an nan iyayenta za su shimfiɗa zanen a gaban dattawan garin,
And, lo, he hath laid an accusation [against her], saying, I have found no tokens of virginity in thy daughter; and yet these are the tokens of my daughter's virginity; and they shall spread the cloth before the elders of the city.
18 dattawan kuwa za su ɗauki mutumin su hukunta shi.
And the elders of that city shall take that man and chastise him;
19 Za su ci masa tara shekel azurfa ɗari, su ba mahaifin yarinyar, domin wannan mutum ya ba wa budurwa mutuniyar Isra’ila mummunan suna. Za tă ci gaba da zama matarsa; ba kuwa zai sake ta ba muddin ransa.
And they shall amerce him in a hundred shekels of silver, and give them unto the father of the damsel; because he hath spread abroad an evil name upon a virgin of Israel; and she shall remain his wife; he shall not be at liberty to put her away all his days.
20 Amma fa in zarge gaskiya ne, ba a kuwa sami shaidar budurcin yarinyar ba,
But if this thing was true, there have not been found tokens of virginity in the damsel:
21 sai a kawo ta a ƙofar gidan mahaifinta, a can mazan gari za su jajjefe ta da dutse har tă mutu. Ta yi abin kunya a Isra’ila ta wurin lalaci a yayinda take a gidan mahaifinta. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
Then shall they lead out the damsel to the door of her father's house, and the men of her city shall stone her with stones that she die; because she hath wrought a disgraceful deed in Israel, to commit incest in her father's house; and thou shalt put away the evil from the midst of thee.
22 In aka kama wani yana kwance da matar wani, dole a kashe dukansu biyu, wato, mutumin da ya kwana da matar da kuma matar. Dole a fid da mugu daga Isra’ila.
If a man be found lying with a woman married to a husband: then shall both of them die, the man that lieth with the woman, and the woman; and thou shalt put away the evil from Israel.
23 In mutum ya sadu da budurwa a gari wadda aka yi alkawarin aure, ya kuma kwana da ita
If a damsel that is a virgin be betrothed unto a man, and a man find her in the city, and lie with her:
24 sai ku ɗauki su biyu zuwa ƙofar wannan gari, ku jajjefe su da dutse har su mutum, za a kashe yarinyar domin tana a cikin gari ba ta kuwa yi ihu neman taimako ba, za a kashe mutumin domin ya yi lalata da matar wani. Dole ku fi da mugu daga cikinku.
Then shall ye lead them both out unto the gate of that city, and ye shall stone them with stones that they die; the damsel, because she cried not [for aid] in the city; and the man, because he hath done violence to his neighbor's wife; and thou shalt put away the evil from the midst of thee.
25 Amma in a bayan gari ne mutumin ya sadu da yarinyar da aka yi alkawari aure, ya kuma yi mata fyaɗe, mutumin da ya yi wannan ne kaɗai zai mutu.
But if in the field the man should find the betrothed damsel, and the man take hold of her by force, and lie with her: then shall the man that lay with her die alone;
26 Kada ku yi wa yarinyar kome, ba tă yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Wannan batu ya yi kamar da na mutumin da ya fāɗa wa maƙwabcinsa ya kuma kashe shi.
But unto the damsel shalt thou not do any thing; there is in the damsel no sin worthy of death; for as when a man riseth against his neighbor, and striketh him dead. even so is this matter;
27 Tun da ya same ta a jeji ne, wataƙila yarinyar ta yi kukan neman taimako, amma babu wani da zai cece ta.
For in the field did he find her; had the betrothed damsel even cried, there would have been none to aid her.
28 In mutum ya sadu da yarinyar da ba a yi alkawarin aurenta ba, ya kuma yi mata fyaɗe, aka kuma kama su,
If a man find a damsel that is a virgin, who is not betrothed, and lay fast hold on her, and lie with her, and they be found:
29 sai yă biya mahaifin yarinyar shekel hamsin na azurfa. Dole yă auri yarinyar, gama ya yi lalata da ita. Ba zai taɓa sake ta ba muddin ransa.
Then shall the man who lieth with her give unto the father of the damsel fifty shekels of silver; and she shall become his wife, because he hath done violence to her, he shall not be at liberty to put her away all his days.
30 Kada mutum yă auri matar mahaifinsa, kada yă ƙasƙantar gādon mahaifinsa.
A man shall not take his lather's wife, and he shall not uncover his father's skirt.

< Maimaitawar Shari’a 22 >