< Maimaitawar Shari’a 21 >
1 In aka sami an kashe mutum kwance a fili, a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, ba a kuma san wanda ya kashe shi ba,
Če je nekdo najden ubit na polju, ki ti ga Gospod, tvoj Bog, daje v last, ležeč na polju in se ne ve kdo ga je umoril,
2 sai dattawanku da alƙalanku su je su gwada nisan wurin da gawar take zuwa garuruwan da suke maƙwabtaka.
potem bodo prišli tvoje starešine in tvoji sodniki in bodo izmerili [razdaljo] do mest, ki so naokoli tega, ki je umorjen.
3 Sai dattawan garin da suke kurkusa da gawar su ɗauki karsanar da ba a taɓa yin aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba,
Zgodilo se bo, da mesto, ki je bliže umorjenemu človeku, celo starešine tega mesta bodo vzeli telico, s katero še niso delali in ki še ni vlekla jarma,
4 a gangara da ita kwarin da ba a taɓa nome, ko shuki a ciki ba, inda kuma akwai rafi mai gudu, a can cikin kwarin za su karye wuyanta.
in starešine tega mesta bodo telico privedli dol v valovito dolino, ki ni niti obdelana niti posejana in tam, v dolini, bodo telici zlomili vrat
5 Firistoci,’ya’yan Lawi maza, za su fito, gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su su yi masa hidima, su kuma furta albarku a cikin sunan Ubangiji, za su kuma daidaita duk rigimar cin mutunci.
in duhovniki, sinovi Lévijevcev, se bodo približali, kajti njih je Gospod, tvoj Bog, izbral, da mu služijo in da blagoslavljajo v Gospodovem imenu, in po njihovi besedi bo vsaka polemika in vsak udarec preizkušen
6 Sa’an nan dukan dattawan garin da yake kurkusa da gawar za su wanke hannuwansu a bisa karsanan da aka karye wuyar a kwarin,
in vse starešine tega mesta, ki je bliže umorjenemu človeku, si bodo roke umili nad telico, ki je obglavljena v dolini
7 za su kuma furta, “Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga an yi haka ba.
in odgovorili bodo ter rekli: ›Naše roke niso prelile te krvi niti naše oči tega niso videle.
8 Karɓi wannan kafara saboda mutanenka Isra’ila, wanda ka fansar, ya Ubangiji, kada kuma ka ɗaura wa mutanenka alhakin jinin mutumin nan marar laifi.” Za a kuwa yi kafarar zub da jinin da aka yi.
Bodi usmiljen, oh Gospod, svojemu ljudstvu Izraelu, ki si ga odkupil in ne polagaj nedolžne krvi na svoje ljudstvo Izrael, ki je najbliže.‹ In kri jim bo odpuščena.
9 Ta haka za ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga cikinku, da yake kun yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Tako boš izmed sebe odvzel krivdo nedolžne krvi, ko boš storil to, kar je pravilno v Gospodovih očeh.
10 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, sai Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannuwanku kuka kuma kama su a matsayin bayi,
Ko greš naprej v vojno zoper svoje sovražnike in ti jih Gospod, tvoj Bog, izroči v tvoje roke in si jih zajel kot ujetnike
11 in ka ga wata kyakkyawar mace wadda ta ɗauki hankalinka a cikin bayin, za ka iya aure ta tă zama matarka.
in vidiš med ujetniki lepo žensko in imaš do nje poželenje, da bi jo imel za svojo ženo,
12 Ka kawo ta gidanka ka sa tă aske kanta, tă yanka kumbanta
potem jo boš privedel domov, v svojo hišo. Ona si bo obrila svojo glavo in postrigla svoje nohte
13 tă kuma tuɓe tufafin da ta sa sa’ad da aka kama ta. Bayan ta zauna a gidanka ta kuma yi makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata ɗaya cif, sai ka shiga wurinta ka zama mijinta, za tă kuwa zama matarka.
in iz sebe bo odložila oblačila svojega ujetništva in ostala bo v tvoji hiši in cel mesec bo objokovala svojega očeta in svojo mater. Potem boš šel noter k njej in boš njen soprog in ona bo tvoja žena.
14 In ba ka jin daɗinta, ka bar tă tafi inda take so. Ba za ka sayar da ita ko ka yi da ita kamar baiwa ba, da yake ka ƙasƙantar da ita.
In zgodilo se bo, če z njo ne boš imel veselja, potem jo boš pustil oditi kamor ona hoče. Toda, ker si jo ponižal, je nikakor ne boš prodal za denar, iz nje ne boš naredil trgovskega blaga.
15 In mutum yana da mata biyu, yana kuwa ƙaunar ɗaya, ba ya kuma ƙaunar ɗayan, su biyun kuwa suka haifi masa’ya’ya maza, sai ya zamana cewa ɗan farin ya kasance na wadda ba ya ƙauna,
Če ima mož dve ženi, eno ljubljeno in drugo osovraženo in sta mu rodili otroke, obe, ljubljena in osovražena in če je prvorojenec od tiste, ki je bila osovražena,
16 to, a ranar da zai yi faɗa wane ne a cikin’ya’yansa zai riƙe gādon da zai bar musu, kada yă sa ɗan matar da yake ƙauna yă zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan matar da ba ya ƙauna, wanda shi ne ɗan farin.
potem se bo zgodilo, ko daje svojim sinovom podedovati to, kar ima, da ne sme narediti sina ljubljene prvorojenca pred sinom osovražene, ki je zares prvorojenec,
17 Dole yă yarda cewa ɗan matar da ba ya ƙaunar ne ɗan fari, ta wurin ba shi rabo kashi biyu na dukan abin da yake da shi, gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.
temveč bo sina osovražene priznal za prvorojenca s tem, da mu da dvojni delež od vsega, kar ima, kajti on je začetek njegove moči; pravica prvorojenca je njegova.
18 In mutum yana da gagararren ɗa mai tawaye, wanda ba ya biyayya ga mahaifinsa da mahaifiyarsa, ba ya kuma jin su sa’ad da suke horonsa,
Če ima človek trmoglavega in upornega sina, ki noče ubogati glasu svojega očeta ali glasu svoje matere in ko sta ga karala, da ju noče poslušati,
19 mahaifinsa da mahaifiyarsa za su kama shi su kawo shi ga dattawa a ƙofar garinsu.
potem naj ga njegov oče in njegova mati primeta in ga privedeta k starešinam njegovega mesta in k velikim vratom njegovega kraja
20 Za su ce wa dattawan, “Wannan ɗanmu gagararre ne, mai tawaye. Ba ya mana biyayya. Mai zari ne, kuma mashayi.”
in starešinam mesta bosta rekla: ›Ta najin sin je trmoglav in uporen, noče ubogati najinega glasu. Požeruh je in pijanec.‹
21 Sa’an nan dukan mazan garinsa za su jajjefe shi har yă mutu. Dole ku fid da mugu daga cikinku. Dukan Isra’ila kuwa za su ji wannan su kuma ji tsoro.
In vsi ljudje iz njegovega mesta ga bodo kamnali s kamni, da ta umre. Tako boš zlo odstranil proč izmed vas in ves Izrael bo slišal in se bal.
22 In mutum ya yi laifin da ya isa kisa, aka kuwa rataye shi a itace,
Če je moški zagrešil greh, vreden smrti, in bo usmrčen in ga obesiš na drevo,
23 kada ku bar jikinsa a kan itacen yă kwana. Ku tabbata kun binne shi a ranar, domin duk wanda aka rataye a kan itace la’ananne ne ga Allah. Kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
naj njegovo truplo ne ostane vso noč na drevesu, temveč ga boš vsekakor tisti dan pokopal (kajti ta, ki je obešen, je preklet od Boga), da tvoja dežela, ki ti jo Gospod, tvoj Bog, daje za dediščino, ne bo omadeževana.