< Maimaitawar Shari’a 21 >
1 In aka sami an kashe mutum kwance a fili, a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, ba a kuma san wanda ya kashe shi ba,
When there shall be found one slain on the soil which Yahweh thy God is giving unto thee to possess, lying prostrate in the field, —it not being known who smote him,
2 sai dattawanku da alƙalanku su je su gwada nisan wurin da gawar take zuwa garuruwan da suke maƙwabtaka.
then shall thine elders and thy judges go forth, —and measure unto the cities that are round about the slain;
3 Sai dattawan garin da suke kurkusa da gawar su ɗauki karsanar da ba a taɓa yin aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba,
and it shall be that the city that is nearest unto the slain, the elders of that city shall take a heifer of the herd which hath not been wrought with, which hath not drawn in a yoke;
4 a gangara da ita kwarin da ba a taɓa nome, ko shuki a ciki ba, inda kuma akwai rafi mai gudu, a can cikin kwarin za su karye wuyanta.
and the elders of that city shall take down the heifer into a ravine with an everflowing stream, which is neither tilled nor sown, —and shall behead there the heifer in the ravine.
5 Firistoci,’ya’yan Lawi maza, za su fito, gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su su yi masa hidima, su kuma furta albarku a cikin sunan Ubangiji, za su kuma daidaita duk rigimar cin mutunci.
Then shall the priests the sons of Levi come near, for of them, hath Yahweh thy God made choice to wait upon him, and to bless in the name of Yahweh, —and at their bidding, shall be settled every controversy and every punishment;
6 Sa’an nan dukan dattawan garin da yake kurkusa da gawar za su wanke hannuwansu a bisa karsanan da aka karye wuyar a kwarin,
and, all the elders of that city who are nearest unto the slain, shall bathe their hands over the heifer that hath been beheaded in the ravine,
7 za su kuma furta, “Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga an yi haka ba.
and shall respond, and say, —Our hands, shed not this blood, neither did, our eyes, see [the deed].
8 Karɓi wannan kafara saboda mutanenka Isra’ila, wanda ka fansar, ya Ubangiji, kada kuma ka ɗaura wa mutanenka alhakin jinin mutumin nan marar laifi.” Za a kuwa yi kafarar zub da jinin da aka yi.
Be propitious unto thy people Israel whom thou hast redeemed, O Yahweh, and do not impute innocent blood in the midst of thy people Israel. So shall they obtain propitiation for the guilt of shedding blood.
9 Ta haka za ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga cikinku, da yake kun yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
Thou, therefore shalt consume the guilt of shedding innocent blood out of thy midst, —when thou shalt do that which is right in the eyes of Yahweh.
10 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, sai Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannuwanku kuka kuma kama su a matsayin bayi,
When thou shalt go forth to war against thine enemies, —and Yahweh thy God shall deliver them into thy hand and thou shalt take them captive;
11 in ka ga wata kyakkyawar mace wadda ta ɗauki hankalinka a cikin bayin, za ka iya aure ta tă zama matarka.
and shalt see among the captives a woman of beautiful figure, —and shalt have a desire unto her, and wouldest take her to thee to wife,
12 Ka kawo ta gidanka ka sa tă aske kanta, tă yanka kumbanta
then shalt thou bring her into the midst of thy house, —and she shall shave her head and pare her nails;
13 tă kuma tuɓe tufafin da ta sa sa’ad da aka kama ta. Bayan ta zauna a gidanka ta kuma yi makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata ɗaya cif, sai ka shiga wurinta ka zama mijinta, za tă kuwa zama matarka.
and put away the raiment of her captivity from off her, and shall remain in thy house, and bewail her father and her mother for the space of a month, —and after that, mayest thou go in unto her, and be her husband, and she shall be thy wife.
14 In ba ka jin daɗinta, ka bar tă tafi inda take so. Ba za ka sayar da ita ko ka yi da ita kamar baiwa ba, da yake ka ƙasƙantar da ita.
And it shall be, if thou hast no pleasure in her, then shalt thou let her go whither she will but thou shalt not sell, her for silver, —thou shalt not make merchandise of her, because thou hast humbled her.
15 In mutum yana da mata biyu, yana kuwa ƙaunar ɗaya, ba ya kuma ƙaunar ɗayan, su biyun kuwa suka haifi masa’ya’ya maza, sai ya zamana cewa ɗan farin ya kasance na wadda ba ya ƙauna,
When a man shall have two wives—the one beloved and, the other hated, and they have borne him sons, both she that is beloved, and she that is hated, —and it shall be that the firstborn son belongeth to her that is hated,
16 to, a ranar da zai yi faɗa wane ne a cikin’ya’yansa zai riƙe gādon da zai bar musu, kada yă sa ɗan matar da yake ƙauna yă zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan matar da ba ya ƙauna, wanda shi ne ɗan farin.
then shall it be, that in the day when he maketh his sons to inherit that which he hath, he may not treat the son of the beloved, instead of the son of the hated, as the firstborn;
17 Dole yă yarda cewa ɗan matar da ba ya ƙaunar ne ɗan fari, ta wurin ba shi rabo kashi biyu na dukan abin da yake da shi, gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.
but the true firstborn the son of her that is hated, shall he treat as firstborn by giving him double out of all that is found to be his, —for, he, is the beginning of his strength, his, is the right of the firstborn.
18 In mutum yana da gagararren ɗa mai tawaye, wanda ba ya biyayya ga mahaifinsa da mahaifiyarsa, ba ya kuma jin su sa’ad da suke horonsa,
When a man hath a son, rebellious and insulting, who will not hearken to the voice of his father, and to the voice of his mother, —though they chastise him, yet will not hearken unto them,
19 mahaifinsa da mahaifiyarsa za su kama shi su kawo shi ga dattawa a ƙofar garinsu.
then shall his father and his mother, lay hold of him, —and bring him forth unto the elders of his city, and unto the gate of his place;
20 Za su ce wa dattawan, “Wannan ɗanmu gagararre ne, mai tawaye. Ba ya mana biyayya. Mai zari ne, kuma mashayi.”
and shall say unto the elders of his city: This our son, is rebellious and insulting, —he will not hearken unto our voice, —a glutton and a tippler.
21 Sa’an nan dukan mazan garinsa za su jajjefe shi har yă mutu. Dole ku fid da mugu daga cikinku. Dukan Isra’ila kuwa za su ji wannan su kuma ji tsoro.
Then shall all the men of his city stone him with stones that he die, so shalt thou consume the wicked thing out of thy midst, —and, all Israel, shall hear and fear.
22 In mutum ya yi laifin da ya isa kisa, aka kuwa rataye shi a itace,
But when there shall be in any man a sin worthy of death and he is to be put to death, —and thou shalt hang him on a tree,
23 kada ku bar jikinsa a kan itacen yă kwana. Ku tabbata kun binne shi a ranar, domin duk wanda aka rataye a kan itace la’ananne ne ga Allah. Kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
his dead body shall not remain all night upon the tree but thou shalt bury, him on the same day, for a reproach unto God, is he that is hanged, —so shalt thou not make unclean thy soil which Yahweh thy God is giving unto thee for an inheritance.