< Maimaitawar Shari’a 21 >
1 In aka sami an kashe mutum kwance a fili, a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, ba a kuma san wanda ya kashe shi ba,
“When one is found slain, fallen in a field on the ground which your God YHWH is giving to you to possess it, [and] it is not known who has struck him,
2 sai dattawanku da alƙalanku su je su gwada nisan wurin da gawar take zuwa garuruwan da suke maƙwabtaka.
then your elderly and yours [of those] judging have gone out and measured to the cities which [are] around the slain one,
3 Sai dattawan garin da suke kurkusa da gawar su ɗauki karsanar da ba a taɓa yin aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba,
and it has been, the city which [is] near to the slain one, even [the] elderly of that city have taken a heifer of the herd, which has not been worked with, which has not drawn in a yoke,
4 a gangara da ita kwarin da ba a taɓa nome, ko shuki a ciki ba, inda kuma akwai rafi mai gudu, a can cikin kwarin za su karye wuyanta.
and [the] elderly of that city have brought down the heifer to a hard valley, which is not tilled nor sown, and have beheaded the heifer there in the valley.
5 Firistoci,’ya’yan Lawi maza, za su fito, gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su su yi masa hidima, su kuma furta albarku a cikin sunan Ubangiji, za su kuma daidaita duk rigimar cin mutunci.
And the priests, sons of Levi, have come near—for your God YHWH has fixed on them to serve Him and to bless in the Name of YHWH, and by their mouth is every strife and every stroke—
6 Sa’an nan dukan dattawan garin da yake kurkusa da gawar za su wanke hannuwansu a bisa karsanan da aka karye wuyar a kwarin,
and all [the] elderly of that city, who are near to the slain one, wash their hands over the heifer which is beheaded in the valley,
7 za su kuma furta, “Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga an yi haka ba.
and they have answered and said, Our hands have not shed this blood, and our eyes have not seen—
8 Karɓi wannan kafara saboda mutanenka Isra’ila, wanda ka fansar, ya Ubangiji, kada kuma ka ɗaura wa mutanenka alhakin jinin mutumin nan marar laifi.” Za a kuwa yi kafarar zub da jinin da aka yi.
receive atonement for Your people Israel, whom You have ransomed, O YHWH, and do not permit innocent blood in the midst of Your people Israel; and the blood has been pardoned to them,
9 Ta haka za ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga cikinku, da yake kun yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji.
and you put away the innocent blood out of your midst, for you do that which [is] right in the eyes of YHWH.
10 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, sai Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannuwanku kuka kuma kama su a matsayin bayi,
When you go out to battle against your enemies, and your God YHWH has given them into your hand, and you have taken captive its captivity,
11 in ka ga wata kyakkyawar mace wadda ta ɗauki hankalinka a cikin bayin, za ka iya aure ta tă zama matarka.
and have seen a woman of beautiful form in the captivity, and have delighted in her, and have taken [her] to yourself for a wife,
12 Ka kawo ta gidanka ka sa tă aske kanta, tă yanka kumbanta
then you have brought her into the midst of your household, and she has shaved her head, and prepared her nails,
13 tă kuma tuɓe tufafin da ta sa sa’ad da aka kama ta. Bayan ta zauna a gidanka ta kuma yi makokin mahaifinta da mahaifiyarta wata ɗaya cif, sai ka shiga wurinta ka zama mijinta, za tă kuwa zama matarka.
and turned aside the raiment of her captivity from off her, and has dwelt in your house, and lamented her father and her mother [for] a month of days, and afterward you go in to her and have married her, and she has been to you for a wife.
14 In ba ka jin daɗinta, ka bar tă tafi inda take so. Ba za ka sayar da ita ko ka yi da ita kamar baiwa ba, da yake ka ƙasƙantar da ita.
And it has been, if you have not delighted in her, that you have sent her away at her desire, and surely you do not sell her for money; you do not tyrannize over her, because that you have humbled her.
15 In mutum yana da mata biyu, yana kuwa ƙaunar ɗaya, ba ya kuma ƙaunar ɗayan, su biyun kuwa suka haifi masa’ya’ya maza, sai ya zamana cewa ɗan farin ya kasance na wadda ba ya ƙauna,
When a man has two wives, one loved and the other hated, and they have borne sons to him (the loved one and the hated one), and the firstborn son has been to the hated one,
16 to, a ranar da zai yi faɗa wane ne a cikin’ya’yansa zai riƙe gādon da zai bar musu, kada yă sa ɗan matar da yake ƙauna yă zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan matar da ba ya ƙauna, wanda shi ne ɗan farin.
then it has been, in the day of his causing his sons to inherit that which he has, he is not able to declare firstborn the son of the loved one, in the face of the son of the hated one—the firstborn.
17 Dole yă yarda cewa ɗan matar da ba ya ƙaunar ne ɗan fari, ta wurin ba shi rabo kashi biyu na dukan abin da yake da shi, gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.
But the firstborn, son of the hated one, he acknowledges, to give to him a double portion of all that is found with him, for he [is] the beginning of his strength; to him [is] the right of the firstborn.
18 In mutum yana da gagararren ɗa mai tawaye, wanda ba ya biyayya ga mahaifinsa da mahaifiyarsa, ba ya kuma jin su sa’ad da suke horonsa,
When a man has a son apostatizing and being rebellious—he is not listening to the voice of his father and to the voice of his mother, and they have disciplined him, and he does not listen to them—
19 mahaifinsa da mahaifiyarsa za su kama shi su kawo shi ga dattawa a ƙofar garinsu.
then his father and his mother have laid hold on him, and they have brought him out to [the] elderly of his city, and to the gate of his place,
20 Za su ce wa dattawan, “Wannan ɗanmu gagararre ne, mai tawaye. Ba ya mana biyayya. Mai zari ne, kuma mashayi.”
and have said to [the] elderly of his city, Our son—this one—is apostatizing and being rebellious; he is not listening to our voice—a glutton and drunkard.
21 Sa’an nan dukan mazan garinsa za su jajjefe shi har yă mutu. Dole ku fid da mugu daga cikinku. Dukan Isra’ila kuwa za su ji wannan su kuma ji tsoro.
Then all the men of his city have stoned him with stones and he has died, and you have put away the evil out of your midst, and all Israel hears and fears.
22 In mutum ya yi laifin da ya isa kisa, aka kuwa rataye shi a itace,
And when there is a sin in a man [with] a judgment of death, and he has been put to death, and you have hanged him on a tree,
23 kada ku bar jikinsa a kan itacen yă kwana. Ku tabbata kun binne shi a ranar, domin duk wanda aka rataye a kan itace la’ananne ne ga Allah. Kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
his corpse does not remain on the tree, for you certainly bury him in the day—for he who is hanged [becomes] a curse of God—and you do not defile your ground which your God YHWH is giving to you [for] an inheritance.”