< Maimaitawar Shari’a 20 >

1 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
Kad otideš na vojsku na neprijatelja svojega i vidiš konje i kola i narod veæi od sebe, nemoj se uplašiti od njih, jer je s tobom Gospod Bog tvoj, koji te je izveo iz zemlje Misirske.
2 Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
I kad poðete da se pobijete, neka pristupi sveštenik i progovori narodu,
3 Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
I neka im reèe: slušaj Izrailju! vi polazite danas u boj na neprijatelje svoje, neka ne trne srce vaše, ne bojte se i ne plašite se, niti se prepadajte od njih.
4 Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
Jer Gospod Bog vaš ide s vama i biæe se za vas s neprijateljima vašim da vas saèuva.
5 Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
Potom i vojvode neka progovore narodu, i reku: ko je sagradio novu kuæu a nije poèeo sjedjeti u njoj? neka ide, nek se vrati kuæi svojoj, da ne bi poginuo u boju, i drugi poèeo sjedjeti u njoj.
6 Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
I ko je posadio vinograd a još ga nije brao? neka ide, nek se vrati kuæi svojoj, da ne bi poginuo u boju, i drugi ga brao.
7 Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
I ko je isprosio djevojku a još je nije odveo? neka ide, nek se vrati kuæi svojoj, da ne bi poginuo u boju, i drugi je odveo.
8 Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
Još i ovo neka kažu vojvode narodu i reku: ko je strašiv i trne mu srce? neka ide, nek se vrati kuæi svojoj, da ne bi trnulo srce braæi njegovoj kao njemu.
9 Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
I kad vojvode izgovore narodu, onda neka namjeste glavare od èeta pred narod.
10 Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
Kad doðeš pod koji grad da ga biješ, prvo ga ponudi mirom.
11 In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
Ako ti odgovori mirom i otvori ti vrata, sav narod koji se naðe u njemu neka ti plaæa danak i bude ti pokoran.
12 In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
Ako li ne uèini mira s tobom nego se stane biti s tobom, tada ga bij.
13 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
I kad ga Gospod Bog tvoj preda u ruke tvoje, pobij sve muškinje u njemu maèem.
14 Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
A žene i djecu i stoku i što god bude u gradu, sav plijen u njemu, otmi, i jedi plijen od neprijatelja svojih, koji ti da Gospod Bog tvoj.
15 Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
Tako èini sa svijem gradovima, koji su daleko od tebe i nijesu od gradova ovijeh naroda.
16 Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
A u gradovima ovijeh naroda, koje ti Gospod Bog tvoj daje u našljedstvo, ne ostavi u životu nijedne duše žive.
17 Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
Nego ih zatri sasvijem, Heteje i Amoreje i Hananeje i Ferezeje i Jeveje i Jevuseje, kao što ti je zapovjedio Gospod Bog tvoj.
18 In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
Da vas ne nauèe èiniti gadna djela koja èiniše bogovima svojim, i da ne zgriješite Gospodu Bogu svojemu.
19 Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
Kad opkoliš kakav grad i budeš dugo pod njim bijuæi ga da bi ga uzeo, ne kvari drveta njegovijeh sjekirom; jer možeš s njih jesti, zato ih ne sijeci; jer drvo poljsko je li èovjek da uðe u grad ispred tebe?
20 Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.
Nego drveta koja znaš da im se rod ne jede, njih obaljuj i sijeci i gradi zaklon od grada koji se bije s tobom, dokle ne padne.

< Maimaitawar Shari’a 20 >