< Maimaitawar Shari’a 20 >

1 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
Lapho uphuma impi ukumelana lezitha zakho, ube usubona amabhiza lezinqola, labantu abanengi kulawe, ungabesabi; ngoba iNkosi uNkulunkulu wakho ilawe, eyakukhupha elizweni leGibhithe.
2 Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
Njalo kuzakuthi, nxa selisondela empini, umpristi asondele akhulume labantu,
3 Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
athi kubo: Zwana, Israyeli! Selisondela empini lamuhla limelana lezitha zenu; inhliziyo yenu kayingapheli amandla; lingesabi, lingathuthumeli, lingatshaywa luvalo ngenxa yobukhona babo;
4 Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
ngoba iNkosi uNkulunkulu wenu nguye ohamba lani, ukulilwela ezitheni zenu, ukulisindisa.
5 Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
Lenduna zizakhuluma labantu zithi: Ngubani umuntu owakhe indlu entsha ongazanga ayivule? Kahambe abuyele endlini yakhe, hlezi afele empini, lomunye umuntu ayivule.
6 Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
Ngubani-ke umuntu ohlanyele isivini, ongadlanga okwaso? Kahambe abuyele endlini yakhe, hlezi afele empini, lomunye umuntu adle okwaso.
7 Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
Ngubani-ke umuntu ogane umfazi, engakamthathi? Kahambe abuyele endlini yakhe, hlezi afele empini, lomunye umuntu amthathe.
8 Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
Lezinduna zizakhuluma futhi labantu, zithi: Ngubani umuntu owesabayo ophelelwa ngamandla enhliziyweni? Kahambe abuyele endlini yakhe, ukuze inhliziyo zabafowabo zingaphelelwa ngamandla njengenhliziyo yakhe.
9 Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
Kuzakuthi-ke lapho izinduna seziqedile ukukhuluma labantu, bazabeka izinduna zebutho ephondo lwabantu.
10 Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
Ekusondeleni kwakho emzini ukulwa umelene lawo, uzamemezela ukuthula kuwo.
11 In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
Kuzakuthi-ke, uba ukuphendula ngokuthula, ukuvulela, khona bonke abantu abaficwa kuwo bazakuba yizibhalwa kuwe, bakusebenzele.
12 In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
Kodwa uba ungenzi ukuthula lawe, kodwa usilwa lawe, uzawuvimbezela.
13 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
Nxa iNkosi uNkulunkulu wakho iwunikela esandleni sakho, uzatshaya wonke owesilisa wawo ngobukhali benkemba.
14 Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
Kodwa abesifazana labantwanyana, lezifuyo, lakho konke okusemzini, impango yonke yawo, uzaziphangela yona; uzakudla impango yezitha zakho iNkosi uNkulunkulu wakho ekunike yona.
15 Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
Uzakwenza njalo kuyo yonke imizi ekhatshana kakhulu lawe, engeyisiyo yemizi yalezizizwe.
16 Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
Kodwa emizini yalababantu iNkosi uNkulunkulu wakho ekunika yona ukuba yilifa, kawuyikutshiya lutho luphila oluphefumulayo;
17 Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
kodwa uzabatshabalalisa lokubatshabalalisa: AmaHethi lamaAmori, amaKhanani lamaPerizi, amaHivi lamaJebusi, njengokukulaya kwayo iNkosi uNkulunkulu wakho.
18 In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
Ukuze bangalifundisi ukwenza njengazo zonke izinengiso zabo, abazenze kubonkulunkulu babo, ukuthi lone eNkosini uNkulunkulu wenu.
19 Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
Lapho uvimbezela umuzi isikhathi eside, usilwa lawo ukuwuthumba, ungoni izihlahla zawo ngokuzigamula ngehloka, ngoba ungadla okwazo, kodwa ungazigamuli (ngoba isihlahla seganga singesabantu) ukuza phambi kwakho ekuvimbezeleni.
20 Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.
Kuphela izihlahla elizaziyo ukuthi kayisizo izihlahla zokudla, yilezo ongazichitha lokuzigamula ukuze wakhe inqaba yokuvimbezela maqondana lomuzi olwa impi lawe, uze wehlele phansi.

< Maimaitawar Shari’a 20 >