< Maimaitawar Shari’a 20 >

1 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
When you march out to battle against your enemies, and see horses, chariots, and a people more numerous than you, you must not be afraid of them; for Yahweh your God is with you, he who brought you up out of the land of Egypt.
2 Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
When you are about to enter into battle, the priest must approach and speak to the people.
3 Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
He must say to them, 'Listen, Israel, you are going to battle against your enemies. Do not let your hearts faint. Do not fear or tremble. Do not be afraid of them.
4 Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
For Yahweh your God is the one who is going with you to fight for you against your enemies and to save you.'
5 Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
The officers must speak to the people and say, 'What man is there who has built a new house and has not dedicated it? Let him go and return to his house, so that he does not die in battle and another man dedicates it.
6 Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
Is there anyone who has planted a vineyard and has not enjoyed its fruit? Let him go home, so he will not die in battle and another man enjoy its fruit.
7 Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
What man is there who is engaged to marry a woman but has not yet married her? Let him go home so that he does not die in battle and another man marries her.'
8 Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
The officers must speak further to the people and say, 'What man is there who is fearful or fainthearted? Let him go and return to his house, so that his brother's heart does not melt like his own heart.'
9 Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
When the officers have finished speaking to the people, they must appoint commanders over them.
10 Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
When you march up to attack a city, make those people an offer of peace.
11 In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
If they accept your offer and open their gates to you, all the people who are found in it must become forced labor for you and must serve you.
12 In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
But if it makes no offer of peace to you, but instead makes war against you, then you must besiege it,
13 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
and when Yahweh your God gives you victory and puts them under your control, you must kill every man in the town.
14 Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
But the women, the little ones, the cattle, and everything that is in the city, and all its spoil, you will take as booty for yourself. You will consume the booty of your enemies, whom Yahweh your God has given to you.
15 Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
You must act in this way toward all the cities that are very far from you, cities that are not of the cities of these following nations.
16 Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
In the cities of these peoples that Yahweh your God is giving you as an inheritance, you must save alive nothing that breathes.
17 Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
Instead, you must completely destroy them: the Hittite, and the Amorite, the Canaanite, the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite, as Yahweh your God has commanded you.
18 In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
Do this so that they do not teach you to act in any of their abominable ways, as they have done with their gods. If you do, you will sin against Yahweh your God.
19 Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
When you will besiege a city for a long time, as you wage war against it to capture it, you must not destroy its trees by wielding an ax against them. For you may eat from them, so you must not cut them down. For is the tree of the field a man whom you should besiege?
20 Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.
Only the trees that you know are not trees for food, you may destroy and cut down; you will build siege works against the city that makes war with you, until it falls.

< Maimaitawar Shari’a 20 >