< Maimaitawar Shari’a 20 >

1 Sa’ad da kuka tafi yaƙi da abokan gābanku, kuka ga dawakai da kekunan yaƙi da kuma mayaƙan da suka fi ku yawa, kada ku ji tsoronsu, domin Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar zai kasance tare da ku.
“When your [soldiers] go to fight your enemies, and you see that they have many horses and chariots and that their army is much bigger than yours, do not be afraid of them, because Yahweh our God, who brought your [ancestors safely] out of Egypt, will be with you.
2 Sa’ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist yă zo gaba yă yi wa mayaƙan jawabi.
When you are ready to start the battle, the Supreme Priest must stand in front of the troops.
3 Zai ce, “Ku ji, ya Isra’ila, yau kuna gab da kama da abokan gābanku. Kada ku karai, ko ku ji tsoro; kada ku firgita, ko ku yi rawar jiki a gabansu.
He must say to them, ‘You Israeli men, listen to me! Today you are going to fight against your enemies. Do not be timid or afraid [DOU] or tremble or panic [DOU],
4 Gama Ubangiji Allahnku, yana tafe tare da ku, zai yaƙi abokan gābanku dominku, yă ba ku nasara.”
because Yahweh our God will go with you. He will fight your enemies for you, and he will enable you to defeat them.’
5 Hafsoshi za su ce wa mayaƙa, “Ko akwai wanda ya gina sabon gida bai kuma buɗe shi ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă buɗe shi.
Then the army officers must say to the troops, ‘If anyone among you has just built a new house [RHQ] and has not dedicated it [to God], he should go home [and dedicate the house]. If he does not do that, if he dies in the battle, someone else will dedicate the house [and live in it].
6 Ko akwai wani da ya shuka inabi, bai kuwa fara jin daɗinsa ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă ji daɗinsa.
If anyone among you has planted a vineyard and has not yet harvested any grapes from it [RHQ], he should go home. If he [stays here and] dies in the battle, someone else will [harvest the grapes and] enjoy [the wine made from them].
7 Ko akwai wani da aka yi masa alkawarin mata, bai kuwa aure ta ko ba? Bari yă tafi gida, kada yă mutu a yaƙi, wani dabam yă aure ta.”
If anyone among you has become engaged to marry a woman [but has not married her yet] [RHQ], he should go home. If [he stays here and] dies in the battle, someone else will marry her.’
8 Sa’an nan hafsoshin za su ƙara da cewa, “Ko akwai wani da yake tsoro, ko ya karai? Bari yă tafi gida don kada’yan’uwansa su karai su ma.”
“Then the officers must also say, ‘If anyone among you is afraid or timid [RHQ], he should go home, in order that he does not cause his fellow soldiers to also stop being courageous.’
9 Sa’ad da hafsoshin suka gama magana da mayaƙan, sai su naɗa komandodi a kansu.
And when the officers have finished speaking to the troops, they must appoint commanders [to lead the groups of soldiers].
10 Sa’ad da kuka haura don ku fāɗa wa birni, sai ku fara neman garin da salama.
“When you come near a city [that is far away] to attack it, first tell the people there that if they surrender, you will not attack them.
11 In sun yarda da salamar, suka buɗe ƙofofin garinsu, to, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su kuma yi muku aiki.
If they open the gates of the city and surrender, they all will become your slaves to work for you.
12 In kuwa suka ƙi salamar, suka fāɗa muku da yaƙi, sai ku yi wa wannan birni ƙawanya.
But if they refuse to [surrender] peacefully, and decide instead to fight against you, your troops must surround the city [and break through the walls].
13 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba da shi cikin hannunku, sai ku kashe dukan mazan da suke cikinsa da takobi.
Then, when Yahweh our God enables you to capture [IDM] the city, you must kill all the men in the city.
14 Game da mata, yara, dabbobi da kuma sauran abubuwan da suke cikin birnin, za ku iya kwasa waɗannan a matsayin ganima wa kanku. Za ku kuma yi amfani da ganimar da Ubangiji Allahnku ya ba ku daga abokan gābanku.
But you are allowed to take for yourselves the women, the children, the livestock, and everything else [that you want to take] from the city. You will be allowed to enjoy all the things that belonged to your enemies; it is Yahweh our God who has given those things to you.
15 Haka za ku yi da dukan biranen da suke nesa da ku, waɗanda kuma ba na al’ummai da suke kusa ba.
You should do that in all the cities that are far from the land in which you will settle.
16 Amma fa, a cikin biranen al’ummai da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kada ku bar wani abu mai numfashi da rai.
“But in the cities that are in the land that Yahweh our God is giving to you, you must kill all the people and all the animals [LIT].
17 Ku hallaka su ƙaƙaf, wato, Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa, yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku.
You must get rid of them completely. Get rid of the Heth people-group, the Amor people-group, the Canaan people-group, the Periz people-group, the Hiv people-group, and the Jebus people-group; that is what Yahweh our God commanded you to do.
18 In ba haka ba, za su koya muku ku bi dukan abubuwan banƙyaman da suke yi, ta yin sujada wa allolinsu, ta haka kuwa ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi.
If you do not do that, they will teach you to sin against Yahweh our God and do the disgusting things that they do when they worship their gods.
19 Sa’ad da kuka yi wa birni ƙawanya kuka daɗe, kuka yi ta yaƙi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari, domin za ku ci’ya’yansu. Kada ku sassare su. Gama itatuwan da suke cikin gonaki, ba mutane ne da za ku yi musu ƙawanya?
“When you surround a city for a long time, trying to capture it, do not cut down the fruit trees [outside the city]. You are allowed to eat the fruit from the trees, but do not get rid of the trees, because they certainly are not [RHQ] your enemies.
20 Amma fa, za ku iya sassare itatuwan da kuka sani ba sa ba da’ya’ya, ku kuma yi amfani da su don ayyukan gina ƙawanyar, sai an ci birnin da yaƙi.
You are permitted to cut down the other trees and use the wood to make ladders and towers to enable you to [go over the walls and] capture the city.”

< Maimaitawar Shari’a 20 >