< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
Potem smo se obrnili in šli na svoje potovanje v divjino, ob poti Rdečega morja, kakor mi je Gospod govoril in mnogo dni smo obkrožali gorovje Seír.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
In Gospod mi je spregovoril, rekoč:
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
›Dovolj dolgo ste obkrožali to goro, obrnite se proti severu.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
Zapovej ljudstvu, rekoč: ›Šli boste skozi pokrajino svojih bratov, Ezavovih otrok, ki prebivajo v Seírju in oni se vas bodo bali, zato dobro pazite nase.
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
Ne vmešavajte se vanje, kajti ne bom vam dal od njihove dežele, ne, niti za širino stopala ne, ker sem gorovje Seír izročil Ezavu za posest.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
Od njih boste hrano kupovali za denar, da boste lahko jedli in od njih boste tudi vodo kupovali za denar, da boste lahko pili.
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
Kajti Gospod, tvoj Bog, te je blagoslovil pri vseh delih tvoje roke. Pozna tvojo hojo skozi to veliko divjino. Teh štirideset let je bil Gospod, tvoj Bog, s teboj; nikakršnega pomanjkanja nisi trpel.‹‹
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
Ko smo šli mimo svojih bratov, Ezavovih otrok, ki so prebivali v Seírju, skozi pot ravnine od Eláta in od Ecjón Geberja, smo se obrnili in prešli po poti moábske divjine.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
Gospod mi je rekel: ›Moábcev ne spravi v tegobo niti se z njimi ne spoprimi v boju, kajti njihove dežele ti ne bom dal v last, ker sem Ar dal Lotovim otrokom za posest.‹
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
Emejci so v njej prebivali v preteklih časih, veliko, številno in visoko ljudstvo, kakor Anákovci,
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
ki so bili tudi prišteti med velikane, kakor Anákovci, toda Moábci so jih imenovali Emejci.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
Tudi Horéjci so poprej prebivali v Seírju, toda Ezavovi otroci so jih pregnali, ko so jih uničili pred seboj in prebivali namesto njih, kakor je Izrael storil v deželi njihove posesti, ki jim jo je dal Gospod.
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
›Sedaj se vzdignite, ‹ sem rekel ›in se odpravite čez potok Zered.‹ In šli smo preko potoka Zered.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Časa, v katerem smo prišli iz Kadeš Barnée, dokler nismo prešli preko potoka Zered, je bilo osemintrideset let, dokler ni pomrl ves rod bojevnikov izmed vojske, kakor jim je prisegel Gospod.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
Kajti zares je bila Gospodova roka zoper njih, da jih uniči izmed vojske, dokler niso bili použiti.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
Tako se je pripetilo, ko so bili vsi bojevniki izmed ljudstva použiti in mrtvi,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
da mi je Gospod spregovoril, rekoč:
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
›Danes boš prešel skozi Ar, moábsko pokrajino
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
in ko prideš blizu, nasproti Amónovih otrok, jih ne spravi v tegobo niti se ne vmešavaj vanje, kajti od dežele Amónovih otrok ti ne bom dal nobene posesti, ker sem jo dal Lotovim otrokom za posest.‹
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
(Tudi ta je bila šteta [za] deželo velikanov. Tam so v starih časih prebivali velikani. Amónci so jih imenovali Zamzuméjce,
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
veliko, številno in visoko ljudstvo, kakor Anákovci. Toda Gospod jih je uničil pred njimi in oni so jih nasledili in prebivali namesto njih,
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
kakor je storil Ezavovim otrokom, ki so prebivali v Seírju, ko je pred njimi uničil Horéjce. Le-ti so jih nasledili in celo do tega dne prebivali namesto njih.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
Avéjce, ki so prebivali v Haserimu, celó do Gaze, so Kaftorejci, ki so izšli iz Kaftorja, uničili in prebivali namesto njih.)
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
›Dvignite se, pojdite na potovanje in prečkajte reko Arnón. Glej, v tvojo roko sem izročil Amoréjca Sihóna, kralja v Hešbónu in njegovo deželo. Začnite jo jemati v last in se z njim spoprimite v bitki.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
Danes bom začel pred teboj spuščati grozo in strah nad narode, ki so pod celotnim nebom, ki bodo slišali poročilo o tebi in bodo trepetali in bodo zaradi tebe v tesnobi.‹
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
In odposlal sem poslance iz divjine Kedemót k Sihónu, kralju v Hešbónu, z besedami miru, rekoč:
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
›Naj grem skozi tvojo deželo. Šel bom vzdolž visoke poti, ne bom se obrnil niti k desni roki niti k levi.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
Hrano mi boš prodajal za denar, da bom lahko jedel in vodo mi [boš] dajal za denar, da bom lahko pil, samo na svojih stopalih bom šel skozi
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
(kakor so mi storili Ezavovi otroci, ki prebivajo v Seírju in Moábci, ki prebivajo v Aru), dokler ne bom šel čez Jordan v deželo, ki nam jo daje Gospod, naš Bog.‹
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
Toda Sihón, kralj v Hešbónu, nam ni dovolil iti mimo njega, kajti Gospod, tvoj Bog, je zakrknil njegovega duha in njegovo srce naredil trdovratno, da bi ga lahko izročil v tvojo roko, kakor se kaže ta dan.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
Gospod mi je rekel: ›Glej, pred teboj sem ti začel dajati Sihóna in njegovo deželo. Začni jo jemati v last, da boš lahko podedoval njegovo deželo.‹
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
Potem je zoper nas prišel ven Sihón, on in njegovo ljudstvo, da se borijo pri Jahacu.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
Gospod, naš Bog, ga je pred nami izročil in udarili smo njega, njegove sinove in vse njegovo ljudstvo.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
Ob tistem času smo zavzeli vsa njegova mesta in popolnoma uničili moške, ženske in malčke iz vsakega mesta. Nobenega nismo pustili ostati.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
Samo živino smo si vzeli za plen in ukradeno blago mest, ki smo jih zavzeli.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
Od Aroêrja, ki je pri bregu reke Arnón in od mesta, ki je pri reki, celo do Gileáda, tam ni bilo niti enega mesta premočnega za nas. Gospod, naš Bog, jih je vsa izročil nam.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
Samo v deželo Amónovih otrok nisi prišel niti v noben kraj reke Jabók niti v gorska mesta niti v katerakoli, ki nam jih je Gospod, naš Bog, prepovedal.

< Maimaitawar Shari’a 2 >