< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
آنگاه طبق دستور خداوند بازگشتیم و از راهی که به سوی دریای سرخ می‌رود به بیابان رفتیم. سالهای زیادی در اطراف ناحیهٔ کوه سعیر سرگردان بودیم. سرانجام خداوند فرمود:
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
«به اندازهٔ کافی در این کوهستان سرگردان بوده‌اید. حال به سمت شمال بروید.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
به قوم بگو که ایشان از مرز سرزمینی خواهند گذشت که به برادرانشان ادومی‌ها تعلق دارد. (ادومی‌ها از نسل عیسو هستند و در سعیر زندگی می‌کنند.) آنها از شما خواهند ترسید،
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
ولی شما با ایشان نجنگید، چون من تمام سرزمین کوهستانی سعیر را به عنوان ملک دائمی به ایشان داده‌ام و حتی یک وجب از زمین ایشان را به شما نخواهم داد.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
در آنجا به ازای آب و غذایی که مصرف می‌کنید، پول بپردازید.
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
خداوند، خدایتان در تمام چهل سالی که در این بیابان بزرگ سرگردان بوده‌اید با شما بوده و قدم به قدم از شما مراقبت نموده است. او در تمام کارهایتان به شما برکت داده و شما هیچوقت محتاج به چیزی نبوده‌اید.»
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
بنابراین ما از کنار سعیر که برادرانمان از نسل عیسو در آنجا زندگی می‌کردند گذشتیم و جاده‌ای را که به سمت جنوب به اِیلَت و عصیون جابر می‌رود قطع نموده، رو به شمال به طرف بیابان موآب کوچ کردیم.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
آنگاه خداوند به ما چنین هشدار داد: «با موآبی‌ها که از نسل لوط هستند کاری نداشته باشید و با ایشان وارد جنگ نشوید. من شهر عار را به ایشان داده‌ام و هیچ زمینی را از سرزمین ایشان به شما نخواهم داد.»
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
(ایمی‌ها که قبیلهٔ بسیار بزرگی بودند قبلاً در آن ناحیه سکونت داشتند و مثل غولهای عناقی بلند قد بودند.
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
ایمی‌ها و عناقی‌ها غالباً رفائی خوانده می‌شوند، ولی موآبی‌ها ایشان را ایمی می‌خوانند.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
در روزگار پیشین حوری‌ها در سعیر سکونت داشتند، ولی ادومی‌ها یعنی قوم عیسو آنها را بیرون رانده، جایشان را گرفتند، همان‌طور که اسرائیل مردم کنعان را که خداوند سرزمینشان را به اسرائیل بخشیده بود، بیرون راندند.)
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
خداوند فرمود: «اکنون برخیزید و از رود زارَد بگذرید.» ما چنین کردیم.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
سی و هشت سال پیش، ما قادش را ترک گفته بودیم. همان‌طور که خداوند فرموده بود، در این مدت تمام جنگجویان ما از بین رفتند.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
خداوند بر ضد آنها بود و سرانجام همهٔ آنها را از بین برد.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
پس از اینکه تمام جنگجویان مردند
17 sai Ubangiji ya ce mini,
خداوند به من فرمود:
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
«امروز باید از شهر عار که در مرز موآب است بگذرید.
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
وقتی به سرزمین عمونی‌ها که از نسل لوط هستند نزدیک شدید با آنها کاری نداشته باشید و با ایشان وارد جنگ نشوید، زیرا هیچ زمینی را از سرزمینی که به ایشان بخشیده‌ام، به شما نخواهم داد.»
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
(آن ناحیه نیز زمانی محل سکونت رفائی‌ها که عمونی‌ها ایشان را زَمزُمی می‌خوانند، بود.
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
آنها قبیلهٔ بسیار بزرگی بودند و مثل عناقی‌ها قد بلندی داشتند، ولی خداوند ایشان را هنگام ورود عمونی‌ها از بین برد و عمونی‌ها به جای ایشان در آنجا سکونت کردند.
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
خداوند به همین گونه به قوم عیسو در کوه سعیر کمک کرده بود و آنها حوری‌ها را که قبل از ایشان در آنجا سکونت داشتند از بین برده و تا امروز به جای ایشان ساکن شده‌اند.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
وضع مشابه دیگر، زمانی اتفاق افتاد که مردم کفتور به قبیلهٔ عِوی‌ها که تا حدود غزه در دهکده‌های پراکنده‌ای سکونت داشتند حمله نموده، آنها را هلاک کردند و به جای ایشان ساکن شدند.)
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
آنگاه خداوند فرمود: «از رود ارنون گذشته، به سرزمین سیحونِ اموری، پادشاه حشبون داخل شوید. من او را و سرزمینش را به شما داده‌ام. با او بجنگید و سرزمین او را به تصرف خود درآورید.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
از امروز ترس شما را بر دل مردم سراسر جهان می‌گذارم. آنها آوازهٔ شما را می‌شنوند و به وحشت می‌افتند.»
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
سپس از صحرای قدیموت سفیرانی با پیشنهاد صلح نزد سیحون، پادشاه حِشبون فرستادم.
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
پیشنهاد ما این بود: «اجازه دهید از سرزمین شما عبور کنیم. از جادهٔ اصلی خارج نخواهیم شد و به طرف مزارع اطراف آن نخواهیم رفت.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
هنگام عبور برای هر لقمه نانی که بخوریم و هر جرعه آبی که بنوشیم، پول خواهیم داد. تنها چیزی که می‌خواهیم، اجازهٔ عبور از سرزمین شماست.
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
ادومی‌های نسل عیسو که ساکن سعیرند اجازهٔ عبور از سرزمین خود را به ما دادند. موآبی‌ها هم که پایتختشان در عار است همین کار را کردند. ما از راه اردن به سرزمینی که خداوند، خدایمان به ما داده است می‌رویم.»
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
ولی سیحون پادشاه حِشبون موافقت نکرد، زیرا خداوند، خدای شما او را سختدل گردانید تا او را به دست اسرائیل نابود کند، همچنانکه الان شده است.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
آنگاه خداوند به من فرمود: «اکنون به تدریج سرزمین سیحون پادشاه را به شما می‌دهم. پس شروع به تصرف و تصاحب این سرزمین کن.»
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
آنگاه سیحون پادشاه به ما اعلان جنگ داد و نیروهایش را در یاهص بسیج کرد.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
ولی خداوند، خدایمان او را به ما تسلیم نمود و ما او را با تمام پسران و افرادش کشتیم و تمامی شهرهایش را به تصرف خود درآورده، همهٔ مردان و زنان و اطفال را از بین بردیم.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
به غیر از گله‌هایشان، موجود دیگری را زنده نگذاشتیم. این گله‌ها را هم با غنایمی که از تسخیر شهرها به چنگ آورده بودیم با خود بردیم.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
ما از عروعیر که در کنارهٔ درهٔ ارنون است تا جلعاد، همهٔ شهرها را به تصرف خود درآوردیم. حتی یک شهر هم در برابر ما قادر به مقاومت نبود، زیرا خداوند، خدایمان تمامی آنها را به ما داده بود.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
ولی ما به سرزمین بنی‌عمون و به رود یبوق و شهرهای کوهستانی یعنی جاهایی که خداوند، خدایمان قدغن فرموده بود، نزدیک نشدیم.

< Maimaitawar Shari’a 2 >