< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
Så vendte vi om og drog til ørkenen på veien til det Røde Hav, således som Herren hadde sagt til mig; og vi drog i lang tid omkring Se'ir-fjellene.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
Da sa Herren til mig:
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
Lenge nok har I draget omkring disse fjell; vend eder nu mot nord!
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
Og byd folket og si: I drar nu frem gjennem det land som tilhører eders brødre Esaus barn, som bor i Se'ir; og de blir redde for eder, men I skal ta eder vel i akt,
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
så I ikke gir eder i strid med dem; jeg vil ikke gi eder så meget som en fotbredd av deres land, for jeg har gitt Esau Se'ir-fjellene til eiendom.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
Mat skal I kjøpe av dem for penger, så I kan ete, og vann skal I også kjøpe av dem for penger, så I kan drikke;
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
for Herren din Gud har velsignet dig i alt det du har tatt dig fore, han har båret omsorg for dig på din vandring gjennem denne store ørken; i firti år har Herren din Gud nu vært med dig, du har ikke manglet noget.
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
Så drog vi videre, bort fra våre brødre Esaus barn, som bor i Se'ir; vi tok av fra veien som går fra Elat og Esjon-Geber gjennem ødemarken, og vendte oss til en annen kant og drog frem på veien til Moabs ørken.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
Da sa Herren til mig: Du må ikke angripe moabittene og ikke gi dig i strid med dem; jeg vil ikke gi dig noget av deres land til eiendom, for jeg har gitt Lots barn Ar til eiendom.
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
Før i tiden bodde emittene der, et stort og tallrikt folk og høit av vekst likesom anakittene.
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
Også de regnes for kjemper likesom anakittene, og moabittene kaller dem emitter.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
Og i Se'ir bodde før i tiden horittene; men Esaus barn drev dem bort og utryddet dem og bosatte sig der i deres sted, likesom Israel nu har gjort med sitt land, det som Herren har gitt dem til eiendom.
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
Gjør eder nu rede og gå over Sered-bekken! Så gikk vi over Sered-bekken.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Den tid vi var på vandring fra Kades-Barnea, til vi gikk over Sered-bekken, var åtte og tretti år, og da var hele den slekt - alle våbenføre menn - utdød av leiren, som Herren hadde svoret at det skulde gå dem.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
Og Herrens hånd var også mot dem, så han rev dem bort av leiren, til det var ute med dem.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
Da nu alle våbenføre menn var utdød av folket,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
da talte Herren til mig og sa:
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
Du drar nu over Moabs landemerker, gjennem Ar,
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
og du kommer nær Ammons barns land; men du må ikke angripe dem eller gi dig i strid med dem; jeg vil ikke gi dig noget av Ammons barns land til eiendom, for jeg har gitt Lots barn det til eiendom.
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
Også dette land regnes for et land med kjemper; før i tiden bodde kjemper der, og ammonittene kaller dem samsummitter.
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
De var et stort og tallrikt folk og høie av vekst likesom anakittene; men Herren utryddet dem for Ammons barn, så de drev dem bort og bosatte sig der i deres sted.
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
Det samme gjorde han for Esaus barn, som bor i Se'ir; for dem utryddet han horittene, så de drev dem bort og bosatte sig der i deres sted, og siden har de bodd der til denne dag.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
Likedan gikk det med avittene, som bodde i landsbyene like til Gasa; de blev ødelagt av kaftorerne, som kom fra Kaftor og bosatte sig der i deres sted.
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
Gjør eder rede, bryt op og gå over Arnon-åen! Se, jeg har gitt amoritten Sihon, kongen i Hesbon, og hans land i din hånd; gå nu i gang med å innta det, og gi dig i strid med ham!
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
Fra denne dag vil jeg la redsel for dig og frykt for dig komme over alle folk under himmelen; alle som får høre om dig, skal skjelve og beve for dig.
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
Da sendte jeg bud fra ørkenen Kedemot til Sihon, kongen i Hesbon, med fredelige ord og lot si:
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
La mig få dra gjennem ditt land! Jeg vil holde mig på veien, jeg vil ikke vike av, hverken til høire eller til venstre.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
Mat kan du selge mig for penger, så jeg kan ete, og vann kan du også gi mig for penger, så jeg kan drikke. La mig bare få dra igjennem på min fot,
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
likesom Esaus barn, som bor i Se'ir, og moabittene, som bor i Ar, gav mig lov til å gjøre - så jeg kan gå over Jordan til det land som Herren vår Gud gir oss.
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
Men Sihon, kongen i Hesbon, vilde ikke la oss dra gjennem sitt land; for Herren din Gud hadde forherdet hans sinn og gjort hans hjerte hårdt for å gi ham i din hånd, som det kan sees på denne dag.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
Og Herren sa til mig: Se, nu gir jeg Sihon og hans land i din vold; gå nu du i gang med å innta det, så du får hans land i eie.
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
Og Sihon og hele hans folk drog ut mot oss til strid, til Jahas.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
Og Herren vår Gud gav ham i vår vold, og vi slo ham og hans sønner og alt hans folk ihjel.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
Og vi inntok dengang alle hans byer og slo hver by med bann, menn og kvinner og barn; vi lot ikke nogen bli tilbake eller slippe unda.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
Bare feet tok vi til bytte foruten hærfanget fra byene som vi inntok.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
Fra Aroer, som ligger ved bredden av Arnon-åen, og fra byen i dalen og like til Gilead var der ikke en by hvis murer var oss for høie; Herren vår Gud gav dem alle i vår vold.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
Men Ammons barns land kom du ikke nær, hverken landet langsmed Jabbok-åen eller byene i fjellene eller noget annet som Herren vår Gud hadde forbudt oss å ta.

< Maimaitawar Shari’a 2 >