< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
Et, nous étant mis en route, nous partîmes pour le désert, par le chemin de la mer Rouge, comme me l'avait dit le Seigneur, et pendant bien des jours nous contournâmes la montagne de Séir.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
Et le Seigneur me dit:
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
C'est assez côtoyer cette montagne, partez donc et allez vers le septentrion.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
Donne au peuple mes ordres, disant: Vous passerez le long des frontières de vos frères les fils d'Esau, qui habitent en Séir, et ils auront crainte de vous, et ils vous redouteront grandement.
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
Ne leur faites point la guerre, car de leur territoire je ne vous donne pas la longueur d'un pied, parce que j'ai donné pour héritage aux fils d'Esau la montagne de Séir.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
Achetez-leur des vivres à prix d'argent, et mangez; prenez-leur de l'eau à la mesure pour de l'argent, et buvez.
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
Car, le Seigneur notre Dieu t'a béni en tous les travaux de tes mains; considère comment tu as sillonné le grand et redoutable désert. Voici quarante ans que le Seigneur est avec toi, et tu n'as manqué d'aucune chose.
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
Nous passâmes donc près de nos frères les fils d'Esau qui habitent la montagne de Séir, par le chemin d'Araba à partir d'Asion-Gaber, et en faisant un détour, nous arrivâmes sur la route du désert de Moab.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
Et le Seigneur me dit: Ne soyez point hostiles aux Moabites, ne leur faites point la guerre; je ne vous ai rien donné de ce territoire, car j'ai donné Aroer aux fils de Lot pour héritage.
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
Les Ommin l'ont habité les premiers: nation grande et nombreuse, puissante comme ceux d'Enac.
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
Ils seront toujours réputés Raphaïm, comme ceux d'Enac, mais ils ont été nommés Ommin par les Moabites.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
Or, en Seir le Horrhéen habita d'abord, et les fils d'Esau le détruisirent; ils effacèrent cette nation devant eux; et à leur place ils habitèrent Séir, comme Israël a fait en la terre de son héritage, que le Seigneur lui a donnée.
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
Levez-vous donc, partez et côtoyez le vallon de Zared.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Or, nous avons mis trente-huit ans à venir de Cadès-Barné au vallon de Zared, et pendant ce temps toute la génération des hommes en état de porter les armes avait péri dans le camp, comme l'avait juré le Seigneur.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
Et la main du Seigneur était sur eux pour les faire périr au milieu du camp, jusqu'à ce qu'ils eussent succombé.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
Et lorsque les hommes en état de porter les armes eurent péri parmi le peuple,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
Le Seigneur me parla, disant:
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
Tu vas aujourd'hui côtoyer les limites de Moab du côté d'Aroer;
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
Vous serez près des fils d'Ammon; ne leur soyez point hostiles, ne leur faites point la guerre; je ne t'ai rien donné du territoire des fils d'Ammon, car j'ai donné cette terre pour héritage aux fils de Lot.
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
Elle sera réputée terre de Raphaïm, car les Raphaïm ont été ses premiers habitants, et les Ammonites les ont surnommés Zochommin,
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
Nation grande et nombreuse, plus puissante que vous, comme ceux d'Enac. Le Seigneur les a détruits devant les Ammonites; ceux-ci ont pris possession de leur terre, et à leur place, ils l'ont habitée jusqu'à ces temps.
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
Ainsi avait-il fait en faveur des fils d'Esau qui habitent Séir; ceux-ci, ayant effacé devant eux le Horrhéen, ont pris possession de sa terre, et, à sa place, l'ont habitée jusqu'à ce jour.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
Pareillement les Evéens qui demeurent en Asedoth jusqu'à Gaza, et les Cappadociens venus de la Cappadoce, les ont détruits en cette contrée et l'habitent à leur place.
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
Levez-vous donc et partez, passez le long du torrent d'Arnon; je vous livre Séhon l'Amorrhéen, roi d'Esebon, et son territoire; commencez à posséder; engagez la guerre avec lui, aujourd'hui même.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
Commence à jeter la terreur et la crainte de ton nom sur la face de toutes les nations qui sont sous le ciel; que ceux qui entendront ton nom soient troublés, que devant ta face elles ressentent les douleurs de la femme qui enfante.
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
Alors, du désert de Cedamoth, j'envoyai des anciens à Séhon, roi d'Esebon, avec des paroles pacifiques, disant:
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
Je traverserai ton territoire; je suivrai la route sans m'écarter ni à droite ni à gauche.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
Donne-moi à prix d'argent des vivres, et je mangerai; donne-moi pour de l'argent de l'eau, et je boirai; je passerai seulement à pied;
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
Comme me l'ont permis les fils d'Esau qui résident en Seir, et les Moabites qui demeurent en Aroer, afin que j'atteigne le Jourdain pour entrer en la terre que notre Dieu nous a donnée.
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
Et Sehon, roi d'Esebon, ne nous permit pas de passer sur son territoire; car le Seigneur avait obscurci son esprit et endurci son cœur, afin qu'il tombât entre tes mains, comme il advint en ce jour.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
Et le Seigneur me dit: Voilà que je commence par te livrer Sehon, roi d'Esebon, et son territoire; commence toi aussi par prendre possession de sa contrée.
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
Et Sehon, roi d'Esebon, sortit à notre rencontre, avec tout son peuple, pour nous combattre en Jassa.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
Et le Seigneur nous le livra: nous battîmes lui, ses fils, tout son peuple,
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
Et nous nous rendîmes maîtres de ses villes en ce temps-là; nous détruisîmes toutes les villes, nous exterminâmes femmes et enfants, nous n'en laissâmes personne en vie.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
Nous ne prîmes que le bétail et la dépouille des villes.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
Depuis Aroer qui est sur les bords du torrent d'Arnon, et la ville bâtie dans la gorge même, jusqu'aux montagnes de Galaad, il n'y eut point de ville qui nous échappât; le Seigneur notre Dieu nous les livra toutes.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
Mais nous ne nous approchâmes, ni des fils d'Ammon, ni de ce qui borde le torrent de Jaboc, ni des villes de la région montagneuse, selon ce que le Seigneur Dieu nous avait prescrit.

< Maimaitawar Shari’a 2 >