< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
And we yeden forth fro thennus, and camen in to the wildirnesse that ledith to the Reed See, as the Lord seide to me; and we cumpassiden the hil of Seir in long tyme.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
And the Lord seide to me, It sufficith to you to cumpasse this hil;
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
go ye ayens the north.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
And comaunde thou to the puple, and seie, Ye schulen passe bi the termes of youre britheren, the sones of Esau, that dwellen in Seir, and thei schulen drede you.
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
Therfor se ye diligentli, that ye be not moued ayens hem; for Y schal not yyue to you of the land `of hem as myche as the steppe of o foot may trede, for Y yaf the hil of Seir in to the possessioun of Esau.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
Ye schulden bie of hem metis for money, and ye schulen ete; ye schulden drawe, and drynke watir bouyt.
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
Thi Lord God blesside thee in al the werk of thin hondis; he knewe thi weye, hou thou passidist this moste wildirnesse, bi fourti yeer; and thi Lord God dwellide with thee, and no thing failide to thee.
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
And whanne we hadden passid bi oure britheren, the sones of Esau, that dwelliden in Seir, bi the weie of the feeld of Elath, and of Asiongaber, we camen to the weie that ledith in to deseert of Moab.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
And the Lord seide to me, Fiyte thou not ayens Moabitis, nether bigyn thou batel ayens hem, for Y schal not yyue to thee ony thing of the lond `of hem, for Y yaf Ar in to possessioun to `the sones of Loth.
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
Emyn, `that is, griseful men, weren first dwelleris therof, a greet puple, and strong, and so hiy, that thei weren bileued as giantis,
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
of the generacioun of Enachym, and thei weren lijk the sones of Enachym; forsothe Moabitis clepen hem Emyn.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
Forsothe Horreis dwelliden bifore in Seir, and whanne thei weren put out, and weren doon awey, `the sones of Esau dwelliden there, as Israel dide in the lond of his possessioun, which the Lord yaf to hym.
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
Therfor we riseden, that we schulden passe the stronde of Zared, and camen to it.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Sotheli the tyme in whiche we yeden fro Cades Barne `til to the passynge of the stronde of Zared, was of eiyte and thretti yeer, til al the generacioun of `men fiyteris was wastid fro `the castels, as the Lord hadde swore; whos hond was ayens hem,
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
that thei schulden perische fro the myddis of `the castels.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
Forsothe after that alle the fiyteris felden doun,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
the Lord spak to me, and seide,
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
Thou schalt passe to dai the termes of Moab,
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
the cytee, Ar bi name, and thou schalt neiy in the nyy coost of the sones of Amon; be thou war that thou fiyte not ayens hem, nether be moued to batel; for Y schal not yyue to thee of the lond of the sones of Amon, for Y yaf it to the `sones of Loth in to possessioun.
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
It is arettid the lond of giauntis, and giauntis enhabitiden therynne sumtyme, whiche giauntis Amonytis clepen Zonym;
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
a myche puple and greet, and of noble lengthe, as Enachym, whiche the Lord dide awey fro the face of hem,
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
and made hem to dwelle for `tho giauntis, as he dide to the sones of Esau, that dwellen in Seire, `and dide awai Horreis, and yaf to hem the lond `of Horreis, which `the sones of Esau welden `til in to present tyme.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
Also men of Capadocie puttiden out Eueys, that dwelliden in Asseryn, `til to Gaza; which yeden out fro Capadocie, and diden awey Eueis, and dwelliden for hem.
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
Rise ye, and `passe ye the stronde of Arnon; lo! Y haue bitake in `thin hond Seon, king of Esebon, of Amorreis; and his lond bigynne thou `to welde, and smyte thou batel ayens him.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
To dai Y schal bigynne to sende thi drede and strengthe in to puplis that dwellen vndir al heuene, that whanne thi name is herd, thei drede, and tremble bi the maner of wymmen trauelynge of child, and `be holdun with sorewe.
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
Therfor Y sente messangeris fro the wildirnesse of Cademoch to Seon, kyng of Esebon; and Y seide with pesible wordis,
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
We schulen passe thorou thi lond, we schulen go in the comyn weie; we schulen not bowe nether to the riyt side, nether to the left side.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
Sille thow metis `to vs for prijs, that we ete; yif thow watir for money, and so we schulen drynke. Oneli it is that thou graunte passage to vs,
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
as the sones of Esau diden, that dwellen in Seir, and as Moabitis diden, that dwellen in Ar, til we comen to Jordan, and passen to the lond which oure Lord God schal yyue to vs.
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
And Seon, kyng of Esebon, nolde yyue passage `to vs; for thi Lord God made hard his spirit, and made sad in yuel `the herte of hym, that he schulde be bitakun in to thin hondis, as thou seest now.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
And the Lord seide to me, Lo, Y bigan to bitake to thee Seon, and his lond; bigynne thou to welde it.
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
And Seon yede out ayens vs with al his puple to batel in Jasa.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
And oure Lord God bitook hym to vs, and we han smyte hym with hise sones, and al his puple.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
And we token in that tyme alle the citees, whanne the dwelleris of tho citees, men, and wymmen, and children weren slayn; we leften not in hem ony thing,
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
outakun beestis that camen in to the part of men takynge prey, and outakun spuylis of the cytees whiche we tokun.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
Fro Aroer, which is on the brenke of the stronde of Arnon, fro the toun which is set in the valey, `til to Galaad, no town was ether citee, that ascapide oure hondis.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
Oure Lord God bitook alle to vs; outakun the lond of the sones of Amon, to which lond we neiyiden not, and outakun alle thingis that liggen to the stronde of Jeboth, and outakun the citees of the munteyns, and alle places fro whiche oure Lord God forbeed vs.

< Maimaitawar Shari’a 2 >