< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
Then we turned and took our journey into the wilderness by the way to the Sea of Reeds, as Yahweh had spoken to me; we went around Mount Seir for many days.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
Yahweh spoke to me, saying,
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
'You have gone around this mountain long enough; turn northward.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
Command the people, saying, “You are to pass through the border of your brothers, the descendants of Esau, who live in Seir; they will be afraid of you. Therefore be careful
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
not to fight with them, for I will not give you any of their land, no, not even enough for the sole of a foot to step on; for I have given Mount Seir to Esau as a possession.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
You will purchase food from them for money, so that you may eat; you will also buy water from them for money, so that you may drink.
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
For Yahweh your God has blessed you in all the work of your hand; he has known your walking through this great wilderness. For these forty years Yahweh your God has been with you, and you have lacked nothing.”'
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
So we passed by our brothers, the descendants of Esau who live in Seir, away from the Arabah road, from Elath and from Ezion Geber. Then we turned and passed by the way of the wilderness of Moab.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
Yahweh said to me, 'Do not trouble Moab, and do not fight with them in battle. For I will not give you his land for your own possession, because I have given Ar to the descendants of Lot, for their possession.'
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
(The Emites lived there previously, a people as great, as many, and as tall as the Anakim;
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
these also are considered to be the Rephaim, like the Anakim; but the Moabites call them the Emim.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
The Horites also lived in Seir previously, but the descendants of Esau succeeded them. They destroyed them from before them and lived in their place, like Israel did to the land of his possession that Yahweh gave to them.)
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
“'Now rise up and go over the brook Zered.' So we went over the brook Zered.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Now the days from when we came from Kadesh Barnea until we crossed the brook Zered, were thirty-eight years. It was by that time that all that generation of the men fit for fighting were gone from the people, as Yahweh had sworn to them.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
Moreover, the hand of Yahweh was against that generation in order to destroy them from the people until they were gone.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
So it happened, when all the men fit for fighting were dead and gone from among the people,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
that Yahweh spoke to me, saying,
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
'You are today to pass over Ar, the border of Moab.
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
When you come near opposite the people of Ammon, do not trouble them or fight them; for I will not give you any of the land of the people of Ammon as a possession; because I have given it to the descendants of Lot as a possession.'”
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
(That also is considered to be a land of the Rephaim. The Rephaim lived there previously—but the Ammonites call them Zamzummim—
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
a people as great, as many, and as tall as the Anakim. But Yahweh destroyed them before the Ammonites, and they succeeded them and lived in their place.
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
This Yahweh also did for the people of Esau, who live in Seir, when he destroyed the Horites from before them, and the descendants of Esau succeeded them and have lived in their place even until today.
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
As for the Avvites who lived in villages as far as Gaza, the Caphtorim, who came from Caphtor, destroyed them and settled in their place.)
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
“'Now rise up, go on your journey, and pass over the Valley of the Arnon; look, I have given into your hand Sihon the Amorite, king of Heshbon, and his land. Begin to possess it, and fight with him in battle.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
Today I will begin to put the fear and terror of you on the peoples that are under the whole sky; they will hear news about you and will tremble and be in anguish because of you.'
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
I sent messengers from the wilderness of Kedemoth to Sihon, king of Heshbon, with words of peace, saying,
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
'Let me pass through your land; I will go along the highway; I will turn neither to the right hand nor to the left.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
You will sell me food for money, so that I may eat; give me water for money, so that I may drink; only let me pass through on my feet;
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
as the descendants of Esau who live in Seir, and as the Moabites who live in Ar, did for me; until I pass over the Jordan into the land that Yahweh our God is giving us.'
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
But Sihon, king of Heshbon, would not let us pass by him; for Yahweh your God had hardened his mind and made his heart obstinate, that he might defeat him by your might, which he has now done today.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
Yahweh said to me, 'Look, I have begun to deliver up Sihon and his land before you; begin to possess it, in order that you may inherit his land.'
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
Then Sihon came out against us, he and all his people, to fight at Jahaz.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
Yahweh our God gave him over to us and we defeated him and his sons and all his people.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
We took all his cities at that time and completely destroyed every city—men and the women and the little ones; we left no survivor.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
Only the cattle we took as spoils for ourselves, along with the spoil of the cities that we had taken.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
From Aroer, which is on the edge of the Valley of the Arnon, and from the city that is in the valley, all the way to Gilead, there was not a city too high for us. Yahweh our God gave them into our hands.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
It was only to the land of the descendants of Ammon that you did not go, as well as all the side of the Jabbok River, and the cities of the hill country—wherever Yahweh our God had forbidden us to go.

< Maimaitawar Shari’a 2 >