< Maimaitawar Shari’a 2 >

1 Sai muka juya muka kama hanya, muka nufi hamada, ta hanyar Jan Teku yadda Ubangiji ya umarce ni. Da daɗewa muka yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun Seyir.
Тогава се върнахме та пътувахме в пустинята през пътя за Червено море, след както Господ беше ми говорил; и дълго време обикаляхме поляната Сиир.
2 Sai Ubangiji ya ce mini,
После Господ ми говори казвайки:
3 “Kun yi ta yawo kewaye da ƙasar tudun nan da daɗewa; yanzu ku juya, ku nufi arewa.
Доволно се обикаляли тая поляна; върнете се към север.
4 Ka ba wa mutane waɗannan umarnai, ka ce, ‘Kuna gab da wucewa cikin yankin’yan’uwanku, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Za su ji tsoronku, amma ku yi hankali
И заповядай на людете, като им кажеш: Ще минете през пределите на братята си исавците, които живеят в Сиир, и те ще се убоят от вас. За това, внимавайте добре;
5 kada ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wata ƙasa daga cikinsu ba, ba ma wadda za tă iya isa ku sa ƙafarku a kai. Na ba wa Isuwa ƙasar tudu ta Seyir, ta zama tasa.
да се не биете с тях, понеже няма да ви дам от земята им ни една стъпка от нога, защото на Исава дадох поляната Сиир за владение.
6 Duk abincin za ku ci, da ruwan da za ku sha, za ku biya su.’”
С пари да купувате от тях храна за ядене, още и с пари да купувате от тях вода за пиене;
7 Ubangiji Allahnku ya albarkace ku cikin dukan aikin hannuwanku. Ya kiyaye ku cikin tafiyarku a duk fāɗin hamada. Waɗannan shekaru arba’in Ubangiji Allahnku ya kasance tare da ku, ba kuwa kun rasa wani abu ba.
защото Господ твоят Бог те благослови във всичките дела на ръцете ти; познал е пътуването ти през тая голяма пустиня; през тия четиридесет години Господ твоят Бог е бил с тебе; не си останал лишен от нищо.
8 Saboda haka muka ci gaba, muka wuce’yan’uwanmu, zuriyar Isuwa, wanda yake zama a Seyir. Muka bar hanyar Araba, wadda ta haura daga Elat da Eziyon Geber, muka nufi wajen hamadar Mowab.
Така минахме покрай братята си исавците, които живееха в Сиир, през пътя по полето от Елат и от Есион-гавер. Върнахме се та минахме през пътя по Моавската пустиня.
9 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ku dami Mowabawa, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku wani sashe na ƙasarsu ba. Na ba da Ar ga zuriyar Lot, ta zama mallakarsu.”
Тогава Господ ми каза: Да не досаждате на моавците, нито да воювате с тях, защото няма да ти дам да владееш нищо от земята им, понеже на Лотовите потомци дадох Ар за владение.
10 (Emawa, mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa, dā sun zauna a can.
(А по-напред живееха там емимите, люде велики и многочислени и високи като енакимите.
11 Kamar Anakawa, su ma an ɗauka su Refahiyawa ne, amma Mowab suna kiransu Emawa.
И те, като енакимите, се считаха исполини; но моавците ги наричаха емими.
12 Haka ma Horiyawa, a dā sun zauna a Seyir, amma zuriya Isuwa suka kore su. Suka hallaka Horiyawa da suke kafinsu, suka kuma zauna a wurinsu, kamar dai yadda Isra’ila ta yi a ƙasar da Ubangiji ya ba su a matsayin mallaka.)
Също и хорейците живееха по-напред в Сиир; но исавците ги заместиха, изтребиха ги от пред себе си и се заселиха на мястото им, както направи Израил в земята на своето наследство, която им даде Господ.)
13 Ubangiji kuwa ya ce, “Yanzu ku tashi ku ƙetare Kwarin Zered.” Sai muka ƙetare kwarin.
Станете сега та преминете потока Заред. И така, преминахме потока Заред.
14 Dukan shekarun da muka yi a tafiyarmu daga Kadesh Barneya zuwa lokacin da muka ƙetare Kwarin Zered, sun kai shekaru talatin da takwas. A lokacin, wannan tsara gaba ɗaya ta mutanen da suka isa yaƙi sun mutu daga sansani, yadda Ubangiji ya rantse musu.
Времето, през което пътувахме от Кадис-варни догде преминахме потока Заред, беше тридесет и осем години, догде се довърши изсред стана цялото поколение на воюващите мъже, както им се кле Господ.
15 Hannun Ubangiji ya yi gāba da su sai da ya hallaka su ƙaƙaf daga sansani.
Още Господната ръка беше против тях, за да ги изтреби изсред стана догде се довършиха.
16 To, sa’ad da na ƙarshe cikin waɗannan mayaƙa a cikin mutanen ya rasu,
А като се довършиха и измряха всички воюващи мъже изсред людете,
17 sai Ubangiji ya ce mini,
Господ ми говори казвайки:
18 “Yau za ku wuce ta yankin Mowab a Ar.
Днес ти ще преминеш Ар, моавската граница;
19 Sa’ad da kuka iso kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su da yaƙi, gama ba zan ba ku mallakar wata ƙasar da take ta Ammonawa ba. Na riga na ba da ita mallaka ga zuriyar Lot.”
и като се приближиш срещу амонците, не им досаждай нито да воюваш с тях, защото няма да владееш нищо от земята на амонците, понеже на Лотовите потомци я дадох за владение.
20 (Wannan ita ma a ɗauka ta a matsayin ƙasar Refahiyawa waɗanda dā sun zauna a can ne; amma Ammonawa suna ce da su Zamzummawa.
(Също и тя се считаше земя на исполините: исполини по-напред живееха там, а амонците ги наричаха замзумими;
21 Mutane ne masu ƙarfi da kuma yawa, suna kuma da tsayi kamar Anakawa. Ubangiji ya hallaka su daga gaban Ammonawa, waɗanda suka kore su, suka kuma zauna a wurinsu.
люде велики и многочислени и високи, като енакимите; но Господ ги изтреби от пред тях; и те ги заместиха и заселиха се на мястото им;
22 Ubangiji ya yi daidai yadda ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a ƙasar Seyir, sa’ad da ya hallaka Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su, suka zauna a wurinsu. Har wa yau, zuriyar Isuwa ne suke zama a can.
за тях направи, както направи за исавците, които живееха в Сиир, когато изтреби хорейците от пред тях, и те ги заместиха и заселиха се на мястото им, гдето са и до днес;
23 Kusan abu ɗaya ya faru, sa’ad da Kaftorawa daga ƙasar Kaftor suka hallaka Awwiyawa, waɗanda dā suke zaune a yankin ƙauyukan da suke kewaye da Gaza. Suka zauna a wurinsu.)
и кафторците излязоха из Кафтор та изтребиха авейците, които живееха в села дори до Газа, и заселиха се на мястото им.)
24 “Ku fito yanzu ku ƙetare Kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon mutumin Amoriyawa a hannunku, na kuma ba da sarkin Heshbon da ƙasarsa. Ku fara mallake ta, ku kuma yi yaƙi da shi.
Станете, тръгнете и преминете потока Арнон; ето, предавам в ръката ти асорееца Сион, цар на Есевон, и земята му; почни да я завладяваш, и бий се с него.
25 A wannan rana zan fara sa tsoro da fargabanku a kan dukan al’ummai, a ƙarƙashin sama. Za su ji labarinku, za su yi rawan jiki, su kuma damu saboda ku.”
Днес ще почна да всявам трепет и страх от тебе върху всичките племена под цялото небе; като чуят за тебе те ще се разтреперят и ще се ужасяват от тебе.
26 Daga hamadar Kedemot, na aiki’yan saƙo zuwa wurin Sihon sarkin Heshbon, a kan ina neman zaman lafiya, ina cewa,
И изпратих посланици от пустинята Кедемот при есевонския цар Сион с мирни думи, да кажат:
27 “Bari mu wuce cikin ƙasarka. Za mu bi ta kan hanya ne kaɗai; ba za mu ratse dama ko hagu ba.
Нека замина през земята ти; право из друма ще вървя; няма да се отбия ни надясно ни наляво.
28 Ka sayar mana da abincin da za mu ci, da kuma ruwan da za mu sha a farashinsu na azurfa. Ka dai bar mu mu wuce ta ƙasarka kawai,
С пари ще ми продаваш храна, за да ям, и с пари ще ми дадеш вода до пия; само с нозете си да замина,
29 kamar yadda zuriyar Isuwa, waɗanda suke zaune a Seyir, da Mowabawa, waɗanda suke zaune a Ar, suka yardar mana, gama muna so mu ƙetare Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.”
(както ми сториха исавците, които живеят в Сиир, и моавците, които живеят в Ар), догде мина през Иордан в земята, която Господ нашият Бог ни дава.
30 Amma Sihon sarkin Heshbon ya ƙi yă bar mu mu wuce a ciki. Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruhunsa ya taurare don yă ba da shi a hannuwanku kamar yadda ya yi yanzu.
Обаче есевонският цар Сион не склони да заминем през земята му; понеже Господ твоят Бог закорави духа му и вкамени сърцето му, за да го предаде в ръцете ти, както е и до днес.
31 Ubangiji ya ce mini, “Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa gare ku. Yanzu ku fara cinta, ku kuma mallake ƙasarsa.”
А Господ ми рече: Ето, започнах да ти предавам Сиона и земята му; почни да превземаш земята му, за да я наследиш.
32 Sa’ad da Sihon da dukan sojojinsa suka fito don su sadu da mu, a yaƙi, a Yahaz,
Тогава Сион излезе против нас, той и всичките му люде, на бой в Яса.
33 sai Ubangiji Allahnmu ya ba da shi gare mu, muka kuwa buga shi tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa.
И Господ нашият Бог го предаде в ръцете ни; поразихме него, синовете му и всичките му люде.
34 A wannan lokaci mun ci dukan biranensa, muka kuma hallaka su, maza, mata da kuma yara. Ba mu bar wani da rai ba.
В онова време превзехме всичките му градове, и във всеки град изтребихме мъжете, жените и децата; не оставихме да оцелее ни един.
35 Amma muka washe, muka kuma kwasa shanu da kuma ganima daga biranen wa kanmu.
Пленихме за себе си само добитъка и користите на градовете, които превзехме.
36 Ubangiji Allahnmu ya taimake mu muka ci Arower wadda take a gefen Kwarin Arnon, da garin da yake a cikin kwarin, har zuwa Gileyad. Babu garin da ya gaggare mu.
От Ароир, при устието на потока Арнон, и от града, който е в долината, дори до Галаад не се намери град, който можа да устои против нас; Господ нашият Бог предаде всичките пред нас.
37 Amma bisa ga umarnin Ubangiji Allahnmu, ba ku yi kusa da wata ƙasar Ammonawa, ko ƙasar da take gefen kwarin kogin Yabbok, ko kuwa wadda take kewaye da birane cikin tuddai ba.
Само към земята на амонците ти не си се приближил, ни към местата край потока Явок, ни към планинските градове, ни към коя да е страна, която Господ нашият Бог ни бе запретил.

< Maimaitawar Shari’a 2 >