< Maimaitawar Shari’a 19 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
“Tanrınız RAB ülkelerini size vereceği ulusları yok ettiğinde ve siz bu ülkeleri mülk edinip kentlerine ve evlerine yerleştiğinizde,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
Tanrınız RAB'bin mülk edinmek için size vereceği ülkenin ortasında kendiniz için üç kent ayıracaksınız.
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Bu kentlere giden yollar yapacak, Tanrınız RAB'bin mülk olarak size vereceği ülkeyi üç bölgeye ayıracaksınız. Öyle ki, birini öldüren bu kentlerden birine kaçabilsin.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
“Birini öldürüp de canını kurtarmak için oraya kaçan kişiyle ilgili kural şudur: Biri, önceden kin beslemediği komşusunu istemeyerek öldürürse,
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
örneğin odun kesmek üzere komşusuyla ormana gidip ağacı kesmek için baltayı vurduğunda balta demiri saptan çıkar, komşusuna çarpar, komşusu ölürse, ölüme neden olan kişi bu kentlerden birine kaçıp canını kurtarsın.
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
Yoksa ölenin öcünü almak isteyen, öfkeyle öldürenin peşine düşebilir, yol uzunsa yetişip onu öldürebilir. Oysa öldüren kişi, öldürdüğü kişiye karşı önceden bir kini olmadığından, ölümü hak etmemiştir.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
Kendinize üç kent ayırın dememin nedeni budur.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
“Tanrınız RAB'bi sevmek, her zaman O'nun yollarında yürümek için bugün size bildirdiğim bütün bu buyruklara uyarsanız, Tanrınız RAB atalarınıza içtiği ant uyarınca sınırınızı genişletir ve onlara söz verdiği bütün ülkeyi size verirse, kendinize üç kent daha ayırın.
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
Öyle ki, Tanrınız RAB'bin mülk olarak size vereceği ülkede suçsuz kanı dökülmesin ve siz de kan dökmekten suçlu olmayasınız.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
“Komşusuna kin besleyen biri pusuya yatar, saldırıp onu öldürür, sonra da bu kentlerden birine kaçarsa,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
kentinin ileri gelenleri peşinden adam gönderip onu kaçtığı kentten geri getirecekler. Öldürülmesi için, ölenin öcünü almak isteyen kişiye teslim edecekler.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Ona acımayacaksınız. İsrail'i suçsuz kanı dökme günahından arındırmalısınız ki, üzerinize iyilik gelsin.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
“Tanrınız RAB'bin mülk edinmek için size vereceği ülkede payınıza düşen mirasta komşunuzun önceden belirlenen sınırını değiştirmeyeceksiniz.”
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
“Herhangi bir suç ya da günah konusunda birini suçlu çıkarmak için bir tanık yetmez. Her sorun iki ya da üç tanığın tanıklığıyla açıklığa kavuşturulacaktır.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
“Eğer yalancı bir tanık kötü amaçla birini suçlarsa,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
aralarında sorun olan iki kişi RAB'bin önünde kâhinlerin ve o dönemde görevli yargıçların önüne çıkarılmalı.
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
Yargıçlar sorunu iyice araştıracaklar. Eğer tanığın kardeşine karşı yalancı tanıklık yaptığı ortaya çıkarsa,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
kardeşine yapmayı tasarladığını kendisine yapacaksınız. Aranızdaki kötülüğü ortadan kaldırmalısınız.
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Geri kalanlar olup bitenleri duyup korkacaklar; bir daha aranızda buna benzer kötü bir şey yapmayacaklar.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Acımayacaksınız: Cana can, göze göz, dişe diş, ele el, ayağa ayak.”

< Maimaitawar Shari’a 19 >