< Maimaitawar Shari’a 19 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
När Herren din Gud hafver utrotat folket, hvilkets land Herren din Gud dig gifva skall, att du dem intager, och bor i deras städer och husom;
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
Så skall du afskilja dig tre städer i landena, som Herren din Gud dig gifva skall till att intaga;
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Och skall utvälja belägna rum, och skifta dins lands gränsor, som Herren din Gud dig utdelandes varder, i tre delar; att dit må fly den som ett mandråp gjort hafver.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
Och det skall vara saken, att dit skall fly den som ett mandråp gjort hafver, att han må lefva. Om någor slår sina nästa icke med vilja, och hafver tillförene intet hat haft till honom;
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Utan såsom någor ginge med sin nästa i skogen till att hugga ved, och hofve med handene yxena upp till att hugga veden och jernet fölle af skaftet, och råkade hans nästa, så att han blefve död; den skall uti en af dessa städerna fly, och få lefva;
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
På det blodhämnaren icke skall fara efter dråparen, medan hans hjerta förbittradt är, och få fatt på honom, om vägen är lång, och slå hans själ; ändock han till döds icke brutit hafver, efter han tillförene intet hat till honom haft hade.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
Derföre bjuder jag dig, att du afskiljer tre städer.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
Och om Herren din Gud dina landsändar utvidgandes varder, såsom han dina fäder svorit hafver, och gifver dig allt det landet, som han dina fäder lofvat hafver att gifva;
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
Om du annars håller all dessa buden, att du gör derefter, som jag dig bjuder i denna dag, att du älskar Herran din Gud, och vandrar i hans vägar i dina lifsdagar, så skall du ännu tre städer lägga till dessa tre städer;
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
På det oskyldigt blod icke skall utgjutet varda i dino lande, som Herren din Gud dig till arfs gifva skall, och blodskulder komma öfver dig.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
Men om någor hafver hat emot sin nästa, och vaktar efter honom, och han går åstad, och slår honom hans själ ihjäl, och flyr uti en af dessa städer;
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
Så skola de äldste i hans stad sända dit, och låta hemta honom dädan, och få honom i blodhämnarens händer, att han skall dräpas.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Din ögon skola intet skona honom, och skall borttaga oskyldigt blod af Israel, på det att dig må väl gå.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Du skall icke dins nästas råmärke flytta, hvilka förfäderna satt hafva i dinom arfvedel, den du ärfver i landena, som Herren din Gud dig gifvit hafver att intaga.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
Intet vittne skall ensamt framträda emot någon om någor missgerning eller synd, ehvad missgerning det är som man göra kan; utan i tvegge eller tregge vittnes mun skola alla saker stå.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
Om ett vrångt vittne går fram emot någon, till att vittna öfver honom någon öfverträdning;
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
Så skola de både männerna, som saken på gäller, stå för Herranom framför Presterna och domarena, som på den tiden äro;
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
Och domarena skola väl ransakat. Och om det falska vittnet hafver burit falskt vittnesbörd emot sin broder;
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
Så skolen I göra honom, såsom han hade aktat göra sinom broder; på det att du skall skilja den onda ifrå dig;
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Och andre skola det höra och rädas, och icke mer taga sig före sådana ondt stycke göra ibland dig.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Ditt öga skall icke skona honom: själ för själ, öga för öga, tand för tand, hand för hand, fot för fot.

< Maimaitawar Shari’a 19 >