< Maimaitawar Shari’a 19 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
Кад Господ Бог твој потре народе којих земљу даје теби Господ Бог твој, и кад их наследиш и настаниш се по градовима њиховим и по кућама њиховим,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
Одвој три града усред земље своје коју ти даје Господ Бог твој да је наследиш,
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Начини пут, и раздели на троје крајеве земље своје коју ти да Господ Бог твој у наследство, па нека бежи онамо сваки крвник.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
А овако нека буде с крвником који утече онамо, да би остао жив: ко убије ближњег свог нехотице, не мрзевши пре на њ,
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Као кад би ко отишао с ближњим својим у шуму да сече дрва, па би замахнуо секиром у руци својој да посече дрво, а она би спала с држалице и погодила би ближњег његова тако да умре он нека утече у који од тих градова да остане жив,
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
Да не би осветник потерао крвника док му је срце распаљено и да га не би стигао на далеком путу и убио га, премда није заслужио смрт, јер није пре мрзео на њ.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
Зато ти заповедам и велим: три града одвој.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
А кад рашири Господ Бог твој међе твоје као што се заклео оцима твојим, и да ти сву земљу коју је рекао дати оцима твојим,
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
Ако уздржиш и уствориш све ове заповести, које ти ја данас заповедам, да љубиш Господа Бога свог и ходиш путевима Његовим свагда, онда додај још три града осим она три,
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
Да се не пролива крв права у земљи твојој, коју ти Господ Бог твој даје у наследство, и да не буде на теби крв.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
Али ако ко мрзи на ближњег свог и вреба га, и скочи на њ, и удари га тако да умре, а он утече у који од тих градова,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
Онда старешине места његова нека пошаљу и узму га оданде, и предаду га у руке осветнику да се погуби.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Нека га не жали око твоје него скини крв праву с Израиља, да би ти добро било.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Не помичи међе ближњег свог коју поставе стари у наследству твом које добијеш у земљи коју ти Господ Бог твој даје да је наследиш.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
Нека не устаје један сведок на човека ни за како зло и ни за какав грех између свих греха који се чине, него на речима два или три сведока да остаје ствар.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
Ако би устао лажан сведок на кога да сведочи на њега да се одмеће Бога,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
Онда нека стану та два човека, који имају ту распру, пред Господа, пред свештенике и пред судије које буду у то време;
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
И нека добро испитају судије, ако сведок онај буде лажан сведок и лажно сведочи на брата свог,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
Учините му онако како је он мислио учинити брату свом и извади зло из себе,
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Да се остали чувши то боје, и унапред више не чине тако зло усред тебе.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Нека не жали око твоје: живот за живот, око за око, зуб за зуб, руку за руку, ногу за ногу.