< Maimaitawar Shari’a 19 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
Lorsque le Seigneur ton Dieu aura détruit les nations dont il va te livrer la terre, et que tu la posséderas, et que tu habiteras dans les villes et dans les maisons,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
Tu sépareras trois villes au milieu de la terre que le Seigneur ton Dieu te donnera en possession,
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Aplanissant soigneusement la voie; et tu partageras en trois parties égales toute l’étendue de ta terre, afin que le fugitif pour cause d’homicide ait dans le voisinage où pouvoir se réfugier.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
Voici la loi de l’homicide fuyant, dont la vie doit être conservée: Celui qui a frappé son prochain, sans s’en apercevoir, et qui est reconnu pour n’avoir eu hier et avant-hier aucune haine contre lui,
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Mais pour être allé simplement avec lui dans la forêt couper du bois, si en coupant le bois la cognée est échappée de sa main, et que le fer sortant du manche ait frappé son ami et l’ait tué, celui-là se réfugiera dans une des susdites villes, et vivra;
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
De peur que le plus proche parent de celui dont le sang a été versé, excité par sa douleur, ne le poursuive et ne l’atteigne, si le chemin est trop long, et ne frappe l’âme de celui qui ne mérite point la mort, parce qu’il est démontré qu’il n’a eu auparavant aucune haine contre celui qui a été tué.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
C’est pourquoi je t’ordonne de placer les trois villes dans une égale distance entre elles.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
Mais lorsque le Seigneur ton Dieu aura étendu tes limites, comme il l’a juré à tes pères, et qu’il t’aura donné toute la terre qu’il leur a promise,
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
(Si cependant tu gardes ses commandements, et que tu fasses ce qu’aujourd’hui je te prescris: que tu aimes le Seigneur ton Dieu et que tu marches dans ses voies en tout temps) tu ajouteras trois autres villes, et tu doubleras ainsi le nombre des trois susdites villes,
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
Afin qu’un sang innocent ne soit pas versé au milieu de la terre que le Seigneur ton Dieu te donnera pour la posséder, afin que tu ne sois pas coupable de sang.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
Mais si quelqu’un, haïssant son prochain, tend des pièges à sa vie, et que, se levant, il le frappe, et que, celui-ci étant mort, il s’enfuie dans une des susdites villes,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
Les anciens de sa ville enverront, et l’enlèveront du lieu de refuge et le livreront à la main du parent de celui dont le sang a été versé, et il mourra.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Tu n’auras pas pitié de lui, et tu ôteras d’Israël le sang innocent, afin que bien t’arrive.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Tu n’enlèveras, et tu ne déplaceras point les bornes de ton prochain, que des prédécesseurs ont posées dans ta possession que le Seigneur ton Dieu te donnera dans la terre que tu recevras pour la posséder.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
Il ne se présentera point un seul témoin contre quelqu’un, quel que soit son péché et son crime; mais c’est sur la parole de deux ou trois témoins que tout sera avéré.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
S’il s’élève un témoin menteur contre un homme, l’accusant de prévarication,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
Les deux qui sont en cause viendront devant le Seigneur en la présence des prêtres et des juges qu’il y aura en ces jours-là.
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
Et lorsqu’après avoir fait la plus exacte perquisition, ils auront trouvé que le faux témoin a dit contre son frère un mensonge,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
Ils lui rendront ce qu’il avait eu dessein de faire à son frère, et tu ôteras le mal d’au milieu de toi,
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Afin que tous les autres entendant, éprouvent de la crainte, et qu’ils n’osent nullement faire de telles choses.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Tu n’auras point pitié de lui; mais tu exigeras âme pour âme, œil pour œil, dent pour dent, main pour main, pied pour pied.

< Maimaitawar Shari’a 19 >