< Maimaitawar Shari’a 19 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
Quand l'Éternel ton Dieu aura exterminé les nations dont l'Éternel ton Dieu te donne le pays, que tu les auras dépossédées, et que tu demeureras dans leurs villes et dans leurs maisons,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
Tu sépareras trois villes au milieu du pays que l'Éternel ton Dieu te donne pour le posséder;
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Tu établiras des chemins, et tu partageras en trois le territoire de ton pays, que l'Éternel ton Dieu te donnera en héritage; et ce sera afin que tout meurtrier se réfugie là.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
Or, voici comment on procédera envers le meurtrier qui s'y enfuira pour sauver sa vie. Si quelqu'un a frappé son prochain par mégarde, et sans l'avoir haï auparavant;
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Comme si quelqu'un va avec son prochain dans la forêt pour couper du bois, que sa main lance la cognée pour couper le bois, et que le fer s'échappe du manche et rencontre son prochain, en sorte qu'il en meure, cet homme-là s'enfuira dans une de ces villes pour sauver sa vie;
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
De peur que le vengeur du sang ne poursuive le meurtrier pendant que son cœur est échauffé, et qu'il ne l'atteigne, si le chemin était trop long, et ne le frappe à mort, bien qu'il ne soit point digne de mort, parce qu'il ne haïssait point son prochain auparavant.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
C'est pourquoi, je te commande, et te dis: Sépare-toi trois villes.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
Que si l'Éternel ton Dieu étend ton territoire, comme il l'a juré à tes pères, et s'il te donne tout le pays qu'il a promis de donner à tes pères,
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
(Parce que tu auras pris garde à pratiquer tous ces commandements que je te prescris aujourd'hui, d'aimer l'Éternel ton Dieu et de marcher toujours dans ses voies), alors tu ajouteras encore trois villes à ces trois-là;
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
Afin que le sang innocent ne soit pas répandu au milieu de ton pays, que l'Éternel ton Dieu te donne en héritage, et que tu ne sois pas coupable de meurtre.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
Mais lorsqu'un homme qui haïssait son prochain lui aura dressé des embûches, et se sera élevé contre lui, et l'aura frappé à mort, et se sera enfui dans l'une de ces villes,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
Les anciens de sa ville l'enverront tirer de là, et le livreront entre les mains du vengeur du sang, afin qu'il meure.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Ton œil ne l'épargnera point; mais tu ôteras d'Israël le sang de l'innocent, et tu seras heureux.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Tu ne déplaceras point les bornes de ton prochain, que tes prédécesseurs auront plantées, dans l'héritage que tu posséderas au pays que l'Éternel ton Dieu te donne pour le posséder.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
Un seul témoin ne sera point valable contre un homme pour quelque crime et péché que ce soit, quelque péché qu'on ait commis; sur la parole de deux ou de trois témoins, une chose sera valable.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
Quand un faux témoin s'élèvera contre quelqu'un pour l'accuser d'infidélité,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
Les deux hommes qui auront contestation entre eux, comparaîtront devant l'Éternel, devant les sacrificateurs et les juges qui seront en ce temps-là;
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
Et les juges s'informeront exactement; et s'il se trouve que ce témoin soit un faux témoin, qu'il ait déposé faussement contre son frère,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
Vous lui ferez comme il avait dessein de faire à son frère; et tu ôteras le méchant du milieu de toi.
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Et les autres l'entendront et craindront, et ils ne feront plus de semblable méchanceté au milieu de toi.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Ton œil sera sans pitié: vie pour vie, œil pour œil, dent pour dent, main pour main, pied pour pied.