< Maimaitawar Shari’a 19 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
When Yahweh thy God, shall cut off the nations whose land Yahweh thy God is giving thee, —and thou shalt dispossess them, and dwell in their cities and in their houses,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
three cities, shalt thou set apart for thee, —in the midst of thy land which Yahweh thy God is giving thee to possess.
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Thou shalt prepare for thee a way, and shalt divide into three parts the boundary of thy land which Yahweh thy God shall cause thee to inherit, —and it shall be that every manslayer shall flee thither.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
And, this, is the case of the manslayer, who shall flee thither and live, —Whoso shall smite his neighbour unwittingly, he, not having hated him aforetime;
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
as when one entereth with his neighbour into a forest, to fell trees, and his hand fetcheth a stroke with the axe, to cut down the tree, and the head flieth off from the handle, and lighteth upon his neighbour, that he die, he, shall flee into one of these cities, and live;
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
lest the blood redeemer pursue the manslayer because his heart is hot, and overtake him because the way is long, and he smite him so as to take away his life, —he not being worthy of death, seeing that he had not been hating him aforetime.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
For this cause, am I commanding thee saying, —Three cities, shalt thou set apart for thee.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
But, if Yahweh thy God should enlarge thy bounds, as he sware unto thy fathers, —and should give thee all the land, which he spake of giving unto thy fathers;
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
because thou dost observe all this commandment to do it which I am commanding thee to-day, to love Yahweh thy God and to walk in his paths all the days, then shalt thou add unto thee yet three cities, unto these three;
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
that innocent blood may not be shed in the midst of thy land, which Yahweh thy God is giving unto thee as an inheritance, —and so shed-blood be upon thee.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
But, when any man shall be hating his neighbour, and shall lie in wait for him and rise up against him, and smite him so as to take away his life that he dieth, —and shall then flee into one of these cities,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
then shall the elders of his city send and fetch him from thence, —and deliver him into the hand of the blood redeemer that he die;
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
thine eye shall not look with pity upon him, —so shall thou consume the shedding of innocent blood out of Israel and it shall go well with thee.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Thou shalt not move back the boundary of thy neighbour, by which they set bounds at first, —in thine inheritance which thou shall receive in the land which Yahweh thy God is giving thee to possess.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
One witness, shall not rise up, against a man for any iniquity, or for any sin, with regard to any sin that he may commit, —at the mouth of two witnesses or at the mouth of three witnesses, must a matter be establish.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
When there shall rise up a wrongful witness against a man, —to answer against him perversely,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
then shall the two men who are at variance stand before Yahweh, —before the priests and the judges who shall be in those days;
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
and the judges shall make diligent inquisition, —and lo! if the witness be, a false witness and, falsely, have answered against his brother,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
then shall ye do unto him as he had thought to de unto his brother, —so shalt thou consume the wicked thing out of thy midst;
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
and, they who remain shall hear and fear, —and not go on to do again according to this wicked thing, in thy midst:
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
neither shall thine eye pity, —life for life, eye for eye, tooth for tooth, hand for hand, foot for foot.

< Maimaitawar Shari’a 19 >