< Maimaitawar Shari’a 19 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
And when the Lord your God shall have destroyed the nations, which God gives you, [even] the land, and you shall inherit them, and dwell in their cities, and in their houses,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
you shall separate for yourself three cities in the midst of your land, which the Lord your God gives you.
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Take a survey of your way, and you shall divide the coasts of your land, which the Lord your God apportions to you, into three parts, and there shall be there a refuge for every manslayer.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
And this shall be the ordinance of the manslayer, who shall flee there, and shall live, whoever shall have struck his neighbour ignorantly, whereas he hated him not in times past.
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
And whoever shall enter with his neighbour into the thicket, to gather wood, if the hand of him that cuts wood with the axe should be violently shaken, and the axe head falling off from the handle should light on his neighbour, and he should die, he shall flee to one of these cities, and live.
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
Lest the avenger of blood pursue after the slayer, because his heart is hot, and overtake him, if the way be too long, and kill him, though there is to this man no sentence of death, because he hated him not in time past.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
Therefore I charge you, saying, You shall separate for your self three cities.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
And if the Lord shall enlarge your borders, as he sware to your fathers, and the Lord shall give to you all the land which he said he would give to your fathers;
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
if you shall listen to do all these commands, which I charge you this day, to love the Lord your God, to walk in all his ways continually; you shall add for yourself yet three cities to these three.
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
So innocent blood shall not be spilt in the land, which the Lord your God gives you to inherit, and there shall not be in you one guilty of blood.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
But if there should be in you a man hating his neighbour, and he should lay wait for him, and rise up against him, and strike him, that he die, and he should flee to one of these cities,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
then shall the elders of his city send, and take him thence, and they shall deliver him into the hands of the avengers of blood, and he shall die.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Your eye shall not spare him; so shall you purge innocent blood from Israel, and it shall be well with you.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
You shall not move the landmarks of your neighbour, which your fathers set in the inheritance, in which you have obtained a share in the land, which the Lord your God gives you to inherit.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
One witness shall not stand to testify against a man for any iniquity, or for any fault, or for any sin which he may commit; by the mouth of two witnesses, or by the mouth of three witnesses, shall every word be established.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
And if an unjust witness rise up against a man, alleging iniquity against him;
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
then shall the two men between whom the controversy is, stand before the Lord, and before the priests, and before the judges, who may be in those days.
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
And the judges shall make diligent enquiry, and, behold, [if] and unjust witness has borne unjust testimony; [and] has stood up against his brother;
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
then shall you do to him as he wickedly devised to do against his brother, and you shall remove the evil from yourselves.
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
And the rest shall hear and fear, and do no more according to this evil thing in the midst of you.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Your eye shall not spare him: [you shall exact] life for life, eye for eye, tooth for tooth, hand for hand, foot for foot.