< Maimaitawar Shari’a 19 >
1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
Ka Jehova Nyasaye ma Nyasachu oseriembo kendo otieko ogendini ma omiyou pinygi ma udakie,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
to yieruru kendo uket tenge mier madongo adek man e dier pinyno ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou mondo ukaw.
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
Geruru yore kuno kendo upog piny ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou ka girkenino nyadidek, mondo ka ngʼato onego dhano to oring odhi otony kuno.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
Ma e chik moketi ne ngʼama onego wadgi kobothne kendo ok ongʼeyo mi oringo odhi kanyo mondo ores ngimane.
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
Kuom ranyisi ngʼato nyalo dhi kod nyawadgi e bungu mondo gitongʼ yien kendo kongʼayo leye malo mondo otongʼ-go yien, to wi le nyalo bwodhore ma tongʼ ngʼatno manege, ngʼatni nyaka ring dhi e mier mag pondogi mondo ores ngimane.
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
Ka ok kamano to jachul kuor nyalo lawe gi mirima ma juke kakanyo ochwalore, kendo nege kata obedo ni ok owinjore gi tho, nimar notimorene ka ok en-gi paro mar timo mano.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
Ma emomiyo achikou mondo uket tenge mier adekgo ne un uwegi.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
Ka Jehova Nyasaye ma Nyasachu omedo tongʼ mar pinyu, kaka nosingore kokwongʼore ni kwereu, ni obiro miyou pinyni duto kaka nosingorenegi,
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
kendo ka uluwo adimba chike duto ma amiyou kawuono mondo uher Jehova Nyasaye ma Nyasachu mi uwuotho e yorene ndalo duto, to nyaka umed yiero mier adek madongo kuom mago.
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
Timuru ma mondo remo maonge ketho kik chwer e pinyu, ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou kaka girkeni mondo kik ubed joketho kuom chwero remo.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
Ka ngʼato ok dwar wadgi mobutone kokiye kendo mi otho bangʼe oringo kodhi e mier madongo mag tonygi,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
to jodong gwengʼno nyaka ome maduoge ka gole e dala maduongʼno mondo gichiwe e lwet joma chulo kuor mondo onege.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Kik utimne ngʼwono, kendo nyaka ugol e dier jo-Israel richo mar chwero remb ngʼat maonge ketho, eka unudhi maber.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Ka udak e lowo mubiro yudo e piny ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu dwaro miyou mondo ukaw kaka girkeni maru, to kik ngʼato kuomu keth kiewo mane kwereu oketo e kind ngʼato gi wadgi.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
Wach janeno achiel kende ok nyal mi ngʼadne ngʼato bura kuom ketho moro kata richo moro motimo. To wach mantie e kind ji nyaka ngʼere malongʼo ka nitiere joneno ariyo kata adek.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
Ka janeno ma ja-miriambo ochungʼ mondo odonjne ja-mahundu,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
to ji ariyo ma laroregi nyaka chungʼ e nyim Jehova Nyasaye ka jodolo kod jongʼad bura manie tich e kindeno nitie.
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
Jongʼad bura nyaka non wachno malongʼo, to ka janeno oyud ni ja-miriambo kochiwo neno maonge adier ewi owadgi,
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
to timne mana kaka ne odwa timo ne owadgi kendo nyaka ugol tim marachno e dieru.
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Ji modongʼ nowinj wachni mi nobed maluor kendo tim mamonono ok nochak otimre kendo e dieru.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Kik ibed gi tim ngʼwono, to chul ngʼato ngima kar ngima, wangʼ kar wangʼ, lak kar lak, lwedo kar lwedo, kendo tielo kar tielo.