< Maimaitawar Shari’a 18 >

1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
Presterna Leviterna, och hela Levi slägt, skola ingen lott eller arf hafva med Israel; Herrans offer och hans arfvedel skola de äta.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Derföre skola de intet arf hafva ibland deras bröder; ty Herren är deras arf, såsom han dem sagt hafver.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
Och detta skall vara Presternas rättighet af folkena, och af dem som offra, ehvad det är fä eller får, att man skall gifva Prestenom bogen, och båda kindbenen, och våmbena;
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
Och förstlingen af ditt korn, och dinom must, och dine oljo; och förstlingen af din fårs klippning.
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
Förty Herren din Gud hafver utvalt honom utur alla dina slägter, att han stå skall i tjenstene i Herrans Namn, och hans söner evärdeliga.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
Om en Levit kommer utaf någon dina städer, eller eljest af hela Israel, der han en gäst är, och kommer af allo hans själs begärelse, till det rum som Herren utvalt hafver;
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
Att han vill tjena i Herrans sins Guds Namn, såsom alle hans bröder Leviterna, som der stå för Herranom;
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
De skola få lika del till att äta, förutan det han hafver af sina fäders sålda godse.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
När du kommer uti landet, som Herren din Gud dig gifvandes varder, så skall du icke lära göra dens folksens styggelse;
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
Att ingen ibland dig varder funnen, som sin son eller dotter låter gå igenom eld, eller den som är en spåman, eller en dagväljare, eller den som på foglalåt aktar, eller trollkarl;
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
Eller besvärjare, eller en svartkonstig, eller en tecknatydare, eller den der någon dödan frågar.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
Ty den som sådant gör, han är Herranom en styggelse; och för sådana styggelses skull fördrifver dem Herren din Gud för dig.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
Var utan vank inför Herranom dinom Gud.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Ty detta folket, som du intaga skall, lyda de dagväljare och spåmän; men du skall icke så göra Herranom dinom Gud.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
En Prophet, såsom mig, skall Herren din Gud uppväcka dig, utaf dig, och utaf dina bröder; honom skolen I lyda.
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
Såsom du beddes af Herranom dinom Gud i Horeb, på församlingenes dag, och sade: Jag vill icke mer höra Herrans mins Guds röst, och icke mer se den stora elden, att jag icke skall dö.
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Och Herren sade till mig: De hafva väl sagt.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
Jag skall uppväcka dem en Prophet, såsom du äst, utaf deras bröder, och gifva min ord i hans mun; han skall tala till dem allt det jag honom bjuda vill.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
Och den som min ord icke hörer, som han i mitt Namn talandes varder, af honom vill jag utkräfva det.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
Dock om någor Prophete djerfves tala i mitt Namn, det jag honom icke befallt hafver att tala, och den som talar i andra gudars namn, den Propheten skall dö.
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
Om du nu säga ville i ditt hjerta: Huru kan jag märka, hvilket ord Herren icke talat hafver?
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
När den Propheten talar i Herrans Namn, och der varder intet af, och sker intet, så är det det ord, som Herren icke talat hafver. Den Propheten hafver det talat af öfverdådighet: derföre skall du icke frukta dig för honom.

< Maimaitawar Shari’a 18 >