< Maimaitawar Shari’a 18 >

1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
کاهنان و سایر افراد قبیلهٔ لاوی نباید در اسرائیل ملکی داشته باشند. بنابراین شما باید با آوردن قربانیها و هدایا به مذبح خداوند، زندگی ایشان را تأمین کنید.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
کاهنان و لاویان نباید ملکی داشته باشند، زیرا همان‌طور که خداوند وعده داده، خود او میراث ایشان است.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
شانه، دو بناگوش و شکمبهٔ هر گاو و گوسفندی را که برای قربانی می‌آورید به کاهنان بدهید.
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
علاوه بر اینها، نوبر محصول خود یعنی نوبر غلات، شراب تازه، روغن زیتون و همچنین پشم گوسفندان خود را نیز به ایشان بدهید؛
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
زیرا خداوند، خدایتان قبیلهٔ لاوی را از بین تمام قبیله‌ها انتخاب کرده است تا نسل اندر نسل خداوند را خدمت کنند.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
هر فرد لاوی، در هر گوشه‌ای از سرزمین اسرائیل که باشد این حق را دارد که هر وقت بخواهد به مکانی که خداوند به عنوان عبادتگاه خود تعیین می‌کند آمده، به نام یهوه خدای خود خدمت کند، درست مانند دیگر برادران لاوی خود که به طور مداوم در آنجا خدمت می‌کنند.
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
از قربانیها و هدایایی که به لاویان داده می‌شود به او نیز باید سهمی تعلق گیرد، چه محتاج باشد و چه نباشد.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
وقتی به سرزمینی که یهوه خدایتان به شما می‌دهد، وارد شدید، مواظب باشید که از آداب و رسوم نفرت‌انگیز قومهایی که در آنجا زندگی می‌کنند پیروی نکنید.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
مانند آنها فرزندان خود را روی آتش مذبح قربانی نکنید. هیچ‌یک از شما نباید به جادوگری بپردازد یا غیبگویی و رمالی و فالگیری کند و یا ارواح مردگان را احضار نماید.
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
خداوند از تمام کسانی که دست به چنین کارها می‌زنند متنفر است. به سبب انجام همین کارهاست که خداوند، خدایتان این قومها را ریشه‌کن می‌کند.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
شما باید در حضور خداوند، خدایتان پاک و بی‌عیب باشید.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
قومهایی که شما سرزمینشان را تصرف می‌کنید به غیبگویان و فالگیران گوش می‌دهند، ولی یهوه خدایتان به شما اجازه چنین کاری را نمی‌دهد.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
او از میان قوم اسرائیل پیامبری مانند من برای شما خواهد فرستاد و شما باید به او گوش دهید و از او اطاعت کنید.
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
روزی که در دامنهٔ کوه حوریب جمع شده بودید از یهوه خدایتان خواستید که صدای مهیب او را بار دیگر نشنوید و آن آتش هولناک را در بالای کوه نبینید، چون می‌ترسیدید بمیرید.
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
پس خداوند به من فرمود: «درخواست آنها بجاست.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
من از میان آنها پیامبری مانند تو برای ایشان خواهم فرستاد. به او خواهم گفت که چه بگوید و او سخنگوی من نزد مردم خواهد بود.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
هر که به او گوش ندهد و به پیامش که از جانب من است توجه نکند، من خود از او بازخواست خواهم کرد.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
هر پیامبری که به دروغ ادعا کند پیامش از جانب من است، خواهد مرد و هر پیامبری که ادعا کند پیامش از جانب خدایان دیگر است باید کشته شود.»
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
اگر دودل هستید که پیامی از جانب خداوند است یا نه،
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
راه فهمیدنش این است: اگر چیزی که او می‌گوید اتفاق نیفتد، پیام او از جانب خداوند نبوده بلکه ساخته و پرداختهٔ خودش است؛ پس، از او نترسید.

< Maimaitawar Shari’a 18 >