< Maimaitawar Shari’a 18 >
1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
Les Sacrificateurs qui sont de la race de Lévi, même toute la Tribu de Lévi, n'auront point de part ni d'héritage avec le reste d'Israël, [mais] ils mangeront les sacrifices de l'Eternel faits par feu, et son héritage.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Ils n'auront donc point d'héritage entre leurs frères. L'Eternel est leur héritage, comme il leur en a parlé.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
Or c'est ici le droit que les Sacrificateurs prendront du peuple, [c'est-à-dire] de ceux qui offriront quelque sacrifice, soit bœuf, ou brebis, ou chèvre, [c'est] qu'on donnera au Sacrificateur l'épaule, les mâchoires, et le ventre.
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
Tu leur donneras les prémices de ton froment, de ton vin et de ton huile, et les prémices de la toison de tes brebis.
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
Car l'Eternel ton Dieu l'a choisi d'entre toutes les Tribus, afin qu'il assiste pour faire le service au nom de l'Eternel, lui et ses fils, à toujours.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
Or quand le Lévite viendra de quelque lieu de ta demeure, de quelque endroit que ce soit d'Israël où il fasse son séjour, et qu'il viendra selon tout le désir de son âme, au lieu que l'Eternel aura choisi,
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
Il fera le service au nom de l'Eternel son Dieu, comme tous ses frères Lévites, qui assistent en la présence de l'Eternel.
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
Ils mangeront une égale portion avec les autres, outre ce que chacun pourra avoir de ce qu'il aura vendu aux familles de ses pères.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
Quand tu seras entré au pays que l'Eternel ton Dieu te donne, tu n'apprendras point à faire selon les abominations de ces nations-là.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
Il ne se trouvera personne au milieu de toi qui fasse passer par le feu son fils ou sa fille, ni de devin qui se mêle de deviner, ni de pronostiqueur de temps, ni aucun qui use d'augures, ni aucun sorcier;
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
Ni d'enchanteur qui use d'enchantements, ni d'homme qui consulte l'esprit de python, ni de diseur de bonne aventure, ni aucun qui interroge les morts.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
Car quiconque fait ces choses est en abomination à l'Eternel; et à cause de ces abominations l'Eternel ton Dieu chasse ces nations-là de devant toi.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
Tu agiras en intégrité avec l'Eternel ton Dieu.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Car ces nations-là dont tu vas posséder le pays, écoutent les pronostiqueurs, et les devins; mais quant à toi, l'Eternel ton Dieu ne t'a point permis d'agir de la sorte.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
L'Eternel ton Dieu te suscitera un Prophète comme moi d'entre tes frères; vous l'écouterez.
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
Selon tout ce que tu as demandé à l'Eternel ton Dieu en Horeb, au jour de l'assemblée, en disant: Que je n'entende plus la voix de l'Eternel mon Dieu; et que je ne voie plus ce grand feu, de peur que je ne meure.
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Alors l'Eternel me dit: Ils ont bien dit ce qu'ils ont dit.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
Je leur susciterai un Prophète comme toi d'entre leurs frères, et je mettrai mes paroles en sa bouche, et il leur dira tout ce que je lui aurai commandé.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
Et il arrivera que quiconque n'écoutera pas mes paroles, lesquelles il aura dites en mon Nom, je lui en demanderai compte.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
Mais le Prophète qui aura agi si fièrement que de dire quelque chose en mon Nom, que je ne lui aurai point commandé de dire, ou qui aura parlé au nom des autres dieux, ce Prophète-là mourra.
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
Que si tu dis en ton cœur: Comment connaîtrons-nous la parole que l'Eternel n'aura point dite?
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
Quand ce Prophète-là aura parlé au Nom de l'Eternel, et que la chose [qu'il aura prédite] ne sera point, ni n'arrivera point, cette parole sera celle que l'Eternel ne lui a point dite; [mais] le Prophète l'a dite par fierté; ainsi n'aie point peur de lui.