< Maimaitawar Shari’a 18 >
1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
La tribu entière de Lévi, prêtres et lévites, n'aura ni part ni héritage en Israël; ils vivront des oblations au Seigneur, selon leurs services.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Ils n'auront point d'héritage parmi leurs frères; le Seigneur seul est leur héritage, comme il le leur a dit.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
Et voici la loi pour les prêtres, concernant les offrandes du peuple et les sacrifices des veaux ou des brebis: tu donneras au prêtre l'épaule, les joues et la poitrine,
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
Et les prémices de ton blé, de ton vin, de ton huile; tu lui donneras aussi les prémices des rejetons de tes menus troupeaux,
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
Parce que le Seigneur l'a choisi, entre toutes les tribus, pour qu'il se tienne devant le Seigneur Dieu, pour qu'il exerce le sacerdoce, pour que lui et ses fils bénissent en son nom le peuple d'Israël.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
Lorsque le lévite, de l'une des villes qu'il habite, partira au gré de son désir, et viendra au lieu qu'aura choisi le Seigneur,
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
Il servira, au nom du Seigneur son Dieu, comme tous ses frères les lévites qui se tiendront en ce lieu devant le Seigneur.
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
Il mangera la portion qui lui est assignée indépendamment de la vente de ce qui lui revient dans sa famille.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
Lorsque tu seras entré en la terre que le Seigneur ton Dieu te donne, tu n'apprendras pas à imiter les abominations des Gentils.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
Il ne se trouvera parmi vous personne qui, pour purifier son fils ou sa fille, les fasse passer par le feu; qui use de la divination, qui prédise, qui prenne les augures.
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
Tu ne chercheras pas à charmer par des incantations magiques, à devenir sorcier ni interprète des prodiges, à interroger les morts.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
Car quiconque fait ces choses est une abomination pour le Seigneur ton Dieu; c'est à cause de ces abominations que le Seigneur exterminera les Gentils devant ta face.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
Tu seras parfait devant le Seigneur ton Dieu.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Car les nations dont tu vas prendre l'héritage, écoutent les devins et ceux qui prédisent l'avenir, et tu es instruit autrement par le Seigneur ton Dieu.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
Le Seigneur ton Dieu suscitera parmi tes frères un prophète semblable à moi; c'est lui que vous écouterez,
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
Parce que, en Horeb, tu en as fait la demande au Seigneur ton Dieu, le jour de l'Eglise; tu as dit: Que nous ne continuions plus d'entendre la voix du Seigneur notre Dieu, que nous ne voyions plus ce grand feu, de peur que nous ne mourions.
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Et le Seigneur m'a dit: ils ont bien parlé.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
Je susciterai pour eux, parmi leurs frères, un prophète semblable à toi; et je mettrai mes paroles dans sa bouche, et il leur parlera selon ce que je lui prescrirai.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
Et je tirerai vengeance de tout homme qui n'écoutera pas ce que ce prophète lui aura dit en mon nom.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
Tout autre prophète qui sera assez impie pour dire en mon nom une parole que je ne lui aurai point commandé de dire, ou qui parlera au nom d'autres dieux, ce prophète sera mis à mort.
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
Et si tu dis en ton cœur: Comment discernerons-nous la parole que le Seigneur n'aura pas dite?
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
Tout ce qu'aura dit ce prophète au nom du Seigneur et qui n'arrivera pas, qui ne se réalisera pas, n'aura point été dit par le Seigneur. Ce prophète aura parlé dans son impiété: vous ne le recevrez pas.