< Maimaitawar Shari’a 18 >

1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
The Levitical priests, in fact the whole tribe of Levi, will not have a share in the land allotment with the other Israelites. They are to eat from the food offerings presented to the Lord—that is what they are entitled to receive.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
While they don't own land among the other tribes, the Lord takes care of them, as he promised.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
The priests' share of a sacrifice of a bull or a sheep that is brought by the people is as follows. The priests are to be given the shoulder, the jaw, and the insides.
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
You are to provide them with the firstfruits of your grain, new wine, and olive oil, as well as the first wool sheared from your flock.
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
For the Lord your God has chosen Levi and his descendants from all your tribes to stand before him and serve in his name forever.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
If a Levite is convinced he should move from any Israelite town and goes to the place the Lord will choose,
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
then he shall be allowed to serve in the name of the Lord his God like all his fellow Levites who stand there in service before the Lord.
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
They will all receive the same food allowances, despite him having received money from the sale of his father's property.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
Once you enter the country the Lord your God is giving you, don't copy the offensive ways of the nations there.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
There should be no one who sacrifices their son or daughter in the fire, practices divination or fortune-telling, uses magic or sorcery,
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
practices witchcraft, visits a medium or spiritist, or communicates with the dead. Anyone does such things offends the Lord.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
It's because of these offensive things that the Lord your God is driving out the nations before you.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
You are to be innocent of such things in the presence of the Lord your God.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Even though these nations, whose land you will occupy, listen to magicians and fortune-tellers, the Lord your God forbids you to do so.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
The Lord your God will send you a prophet like me from your people. You must listen to him.
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
Remember what you told the Lord your God at Horeb when you were all assembled there. You said, “Please don't let us go on hearing the Lord our God speak to us, or see this terrifying fire anymore! Otherwise we're going to die!”
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Then the Lord told me, “They are right in what they're saying.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
I'm going to send them a prophet like you from their people. I will give him my messages, and he will tell them everything I order him to say.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
I will deal with anyone who does not listen to my message that the prophet speaks in my name.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
However, if any prophet claims to be delivering a message in my name that I have not ordered him to give, or speaks in the name of other gods, that prophet must be executed.”
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
You may be wondering, “How can we be sure that a message hasn't come from the Lord?”
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
When a prophet speaks in the Lord's name and what he says doesn't happen or come true, then that is a not a message from the Lord. The prophet has spoken with contempt for the Lord. Don't be intimidated by him.

< Maimaitawar Shari’a 18 >