< Maimaitawar Shari’a 18 >

1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
Præsterne, Leviterne, hele Levi Stamme skal ikke have Del eller Arv med Israel; de skulle æde Herrens Ildofre og hans Arv.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Og han skal ikke have Arv iblandt sine Brødre; Herren, han er hans Arv, ligesom han har talet til ham.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
Men dette skal være Præsternes Rettighed af Folket, af dem, som ofre Ofret, enten Okse eller Lam, at man skal give Præsten Boven og Kæverne og Kallunet.
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
Det første af dit Korn, din nye Vin og din Olie og den første Uld af dine Faar skal du give ham;
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
thi Herren din Gud har udvalgt ham af alle dine Stammer til at staa og tjene i Herrens Navn, ham og hans Sønner alle Dage.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
Og naar en Levit kommer fra en af dine Porte i hele Israel, hvor han opholder sig, og han kommer efter sin Sjæls fulde Lyst til det Sted, hvilket Herren skal udvælge,
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
og han tjener i Herren sin Guds Navn, ligesom alle hans Brødre, Leviterne, som staa der for Herrens Ansigt:
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
Da skulle de nyde lige Del, foruden hvad han ejer af solgt Gods fra Fædrene.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
Naar du kommer til det Land, hvilket Herren din Gud giver dig, da skal du ikke lære at gøre efter disse Folks Vederstyggeligheder.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
Der skal ikke findes hos dig nogen, som lader sin Søn eller sin Datter gaa igennem Ilden, nogen som omgaas med Spaadom eller er en Dagvælger, eller som agter paa Fugleskrig eller er en Troldkarl,
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
eller som omgaas med Manen, eller som adspørger en Spaamand eller er en Tegnsudlægger, eller som gør Spørgsmaal til de døde.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
Thi hver, som gør disse Ting, er en Vederstyggelighed for Herren, og for disse Vederstyggeligheders Skyld fordriver Herren din Gud dem fra sit Ansigt.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
Du skal være fuldkommen for Herren din Gud.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Thi disse Hedninger, som du skal fordrive, de have hørt efter Dagvælgere og Spaamænd; men sligt har Herren din Gud ikke tilstedet dig.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
En Profet af din Midte, af dine Brødre, ligesom mig, skal Herren din Gud oprejse dig; ham skulle I høre;
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
aldeles som du begærede af Herren din Gud ved Horeb paa Forsamlingens Dag og sagde: Jeg kan ikke blive ved at høre Herren min Guds Røst og ikke ydermere se denne store Ild, at jeg ikke skal dø.
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Da sagde Herren til mig: De have talet vel i det, de have talet.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
Jeg vil oprejse dem en Profet midt ud af deres Brødre, ligesom du er; og jeg vil lægge mine Ord i hans Mund, og han skal tale til dem alt det, som jeg vil befale ham.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
Og det skal ske, at den, som ikke vil høre paa mine Ord, som han skal tale i mit Navn, af ham skal jeg kræve det.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
Men den Profet, som formaster sig til at tale et Ord i mit Navn, som jeg ikke har befalet ham at tale, eller den, som taler i andre Guders Navn, den Profet skal dø.
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
Og om du siger i dit Hjerte, hvorledes kunne vi kende det Ord, som Herren ikke har talet:
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
Naar Profeten taler i Herrens Navn, og det Ord sker ikke, og det kommer ikke: Da er det et Ord, som Herren ikke har talet; den Profet har talet det i Formastelse, du skal ikke grue for ham.

< Maimaitawar Shari’a 18 >