< Maimaitawar Shari’a 18 >

1 Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
Svećenici Levijevci - sve pleme Levijevo - neka nemaju udjela ni baštine s Izraelom; neka žive od žrtava paljenih Jahvi i od njegove baštine.
2 Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Neka, dakle, nemaju baštine među svojom braćom: Jahve je njihova baština, kako im je i rekao.
3 To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
Ovo neka bude svećenička pristojba od naroda - od onih koji žrtve prinose, bilo to goveče ili što od sitne stoke: svećeniku treba dati pleće, vilice i želudac.
4 Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
Davaj mu i prvine od svoga žita, od svoga vina, od svoga ulja i prvine od vune svojih ovaca,
5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
jer je njega odabrao Jahve, Bog tvoj, od svih tvojih plemena; njega i njegove sinove, da zauvijek stoje pred Jahvom, Bogom tvojim, te da obavljaju službu i blagoslivljaju u ime Jahve.
6 Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
Ako bi koji levit što boravi u nekom tvome gradu, bilo gdje u Izraelu, svom dušom zaželio da dođe u mjesto što ga Jahve odabere,
7 Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
može tu službovati u ime Jahve, Boga svoga, kao i druga njegova braća Levijevci koji stoje ondje pred Jahvom.
8 Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
Neka jede jednak dio kao i drugi, bez obzira na prodanu očevinu.
9 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
Kad uđeš u zemlju koju ti daje Jahve, Bog tvoj, nemoj se priučavati na odvratne čine onih naroda.
10 Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
Neka se kod tebe ne nađe nitko tko bi kroz oganj gonio svoga sina ili svoju kćer; tko bi se bavio gatanjem, čaranjem, vračanjem i čarobnjaštvom;
11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
nitko tko bi bajao, zazivao duhove i duše predaka ili se obraćao na pokojnike.
12 Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
Jer tko god takvo što čini gadi se Jahvi; zbog takvih odvratnosti njih i goni ispred tebe Jahve, Bog tvoj.
13 Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
Budi posve vjeran Jahvi, Bogu svome.
14 Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
Narodi koje ćeš naskoro otjerati s posjeda slušaju vračare i gatare, ali tebi to Jahve, Bog tvoj, ne dopušta.
15 Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
Proroka kao što sam ja, iz tvoje sredine, od tvoje braće, podignut će ti Jahve, Bog tvoj: njega slušajte!
16 Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
Posve onako kako si i tražio od Jahve, Boga svoga, na Horebu, na dan zbora, kada si govorio: 'Neću više da slušam glas Jahve, Boga svoga, niti želim više gledati taj silni oganj da ne poginem!'
17 Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
Nato mi reče Jahve: 'Pravo su rekli.
18 Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
Podignut ću im proroka između njihove braće, kao što si ti. Stavit ću svoje riječi u njegova usta da im kaže sve što mu zapovjedim.
19 Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
A ne bude li tko poslušao mojih riječi što ih prorok bude govorio u moje ime, taj će odgovarati preda mnom.
20 Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
A prorok koji bi se usuđivao govoriti što u moje ime što ja ne budem zapovjedio da govori i koji bi govorio u ime drugih bogova, takav prorok neka se pogubi.'
21 Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
Možda ćeš reći u svome srcu: 'Kako ćemo raspoznati riječ koju Jahve nije izrekao?'
22 In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.
Kad prorok govori u ime Jahve pa to ne bude i riječ se ne ispuni, onda je to riječ koje Jahve nije kazao. U drskosti je taj prorok govorio. Nemoj od njega strahovati.

< Maimaitawar Shari’a 18 >