< Maimaitawar Shari’a 17 >

1 Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
“Tanrınız RAB'be herhangi bir özürü, kusuru olan sığır ya da koyun kurban etmeyeceksiniz. Tanrınız RAB bundan tiksinir.
2 In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
“Tanrınız RAB'bin size vereceği kentlerin birinde aranızdan O'nun antlaşmasını çiğneyip gözünde kötü olanı yapan bir erkek ya da kadın çıkar
3 wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
ve buyruklarıma aykırı olarak gidip başka ilahlara tapar, onların, güneşin, ayın ya da gök cisimlerinin önünde eğilirse
4 in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
ve bu olay size bildirilirse, duyduklarınızı iyice araştırın. Duyduklarınız doğruysa ve bu iğrenç olayın İsrail'de yapıldığı kanıtlanırsa,
5 sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
bu kötülüğü yapan erkeği ya da kadını kentinizin kapısına çıkarın ve taşa tutarak öldürün.
6 Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
Ölmesi gereken, iki ya da üç kişinin tanıklığıyla öldürülecek; bir kişinin tanıklığıyla öldürülmeyecek.
7 Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
O kişiyi önce tanıklar, sonra bütün halk taşa tutsun. Aranızdaki kötülüğü ortadan kaldırmalısınız.
8 In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
“Eğer kentlerinizde adam öldürme, dava, saldırı konusunda yargılamada sizi aşan sorunlarla karşılaşırsanız, Tanrınız RAB'bin seçeceği yere gidin.
9 Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
Sorunlarınızı Levili kâhinlere ve o dönemde görevli yargıca götürüp soruşturun. Yargı kararını onlar size bildirecekler.
10 Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
RAB'bin seçeceği yerden size bildirilen karara uymalı, size verilen öğüdü tutmaya dikkat etmelisiniz.
11 Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
Size öğretilen yasa ve verilen karar uyarınca davranın. Size bildirilenin dışına çıkmayın.
12 Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
Orada, Tanrınız RAB'bin önünde görev yapan kâhini ya da yargıcı kim dinlemeyip saygısızlık ederse öldürülmeli. İsrail'den kötülüğü atmalısınız.
13 Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
Bütün halk bunu duyup korkacak, bir daha saygısızlık etmeye kalkışmayacaktır.”
14 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
“Tanrınız RAB'bin size vereceği ülkeye girip orayı mülk edinerek yerleştiğinizde ve, ‘Çevremizdeki ulusların tümü gibi biz de başımıza bir kral atayalım’ dediğinizde,
15 ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
atayacağınız kral Tanrınız RAB'bin seçtiği kişi olmalıdır. Atayacağınız kral kendi kardeşlerinizden biri olmalı. Soydaşlarınızdan olmayan birini, bir yabancıyı kral seçmeyeceksiniz.
16 Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
Kral çok sayıda at edinmemeli, daha çok at satın almak için halkı Mısır'a göndermemeli. Çünkü RAB size, ‘Bir daha o yoldan dönmeyeceksiniz’ dedi.
17 Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
Atayacağınız kral yüreğinin RAB'den sapmaması için çok kadın edinmemeli, büyük ölçüde altın, gümüş biriktirmemeli.
18 Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
“Kral tahtına oturunca, Levili kâhinlerin koruması altındaki Kutsal Yasa'nın bir örneğini kendisi bir kitaba yazacak.
19 Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
Bu yasa örneğini yanında bulunduracak, yaşamı boyunca her gün onu okuyacak. Öyle ki, Tanrısı RAB'den korkmayı, bu yasanın bütün sözlerine ve kurallarına uymayı öğrensin;
20 don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.
kendini kardeşlerinden üstün saymasın, yasanın dışına çıkmasın; kendinin ve soyunun krallığı İsrail'de uzun yıllar sürsün.”

< Maimaitawar Shari’a 17 >