< Maimaitawar Shari’a 17 >

1 Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
“Do not sacrifice to Yahweh our God any cattle or sheep or goats that have any defects, because Yahweh hates that kind of gift.”
2 In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
“When you are living in any of the towns [in the land] that Yahweh our God is giving to you, suppose you hear that there is some man or woman who sins by disobeying the agreement that Yahweh has made with you.
3 wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
Suppose someone tells you that that person has worshiped and served other gods, or the sun, or the moon, or the stars.
4 in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
If you hear that some person has been doing that, you must investigate it thoroughly. If [you find out that] it is true that this detestable thing has happened in Israel,
5 sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
you must take outside the town the man or woman who has done it. Then you must kill that person by throwing stones at him or her.
6 Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
But you are allowed to execute such people only if at least two witnesses testify that they saw them [doing that]. They must not be executed if there is only one witness.
7 Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
The (witnesses/ones who saw them doing it) must be the first ones to throw stones at them. Then the other people [MTY] [should throw stones at them]. By doing that, you will get rid of this evil practice among you.”
8 In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
“Sometimes it will be very difficult for a judge to decide what really happened. He might be trying to decide whether, when someone injured or killed another person, he did it accidentally or deliberately. Or he might be trying to decide if some person is suing another person unfairly. If in some town it is very difficult to know what really happened, with the result that the judge cannot decide it, you should go to the place that Yahweh our God has chosen for you [to worship him].
9 Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
There you should present the case to the descendants of Levi who are the priests, and to the judge who is serving at that time, and they should decide what should be done.
10 Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
After they make their decision, you must do what they tell you to do.
11 Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
Accept what they have decided, and do what they say that you should do. Do not try to change in any way what they have decided [IDM].
12 Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
You must execute anyone who proudly/arrogantly disobeys the judge or the priest who stands there in the presence of Yahweh [and decides what should be done]. By doing that, you will get rid of evil practices among you.
13 Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
Then [after that person is executed], all the people will hear about it, and they will be afraid, and none of them will act that way any more.”
14 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
“[I know that] after you have occupied the land that Yahweh our God is giving to you, and you are living there, you will say, ‘We should have a king to rule over us, like the kings that other nations around us have.’
15 ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
Yahweh our God will permit you to have a king, but be sure that you appoint someone whom he has chosen. That man must be an Israeli; you must not appoint someone who is a foreigner to be your king.
16 Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
[After he becomes the king], he should not acquire a large number of horses for himself. He should not send people to Egypt to buy horses for him, because Yahweh said to you, ‘Never return to Egypt [for anything’]!
17 Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
And he must not have a lot of wives, because if he did that, they would turn him [SYN] away from [worshiping only] Yahweh. And he must not acquire a lot of silver and gold.
18 Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
“When he becomes your king, he must [appoint someone to] copy these laws. He must copy them from the scroll that is kept by the priests who are descended from Levi.
19 Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
He must keep this new scroll near him and read from it every day of his life, in order that he may learn to revere Yahweh, and to faithfully obey [DOU] all the rules and regulations [that are written] in these laws.
20 don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.
If he does that, he [SYN] will not think that he is (better/more important) than [IDM] his fellow Israelis, and he will completely obey [LIT] Yahweh’s commands. As a result, he and his descendants will rule as kings in Israel for many years.”

< Maimaitawar Shari’a 17 >