< Maimaitawar Shari’a 16 >
1 Ku kiyaye watan Abib, ku kuma yi shagalin Bikin Ƙetarewar Ubangiji Allahnku, domin a watan Abib ne ya fitar da ku daga Masar da dad dare.
Observe the month of new corn, which is the first of the spring, that thou mayst celebrate the phase to the Lord thy God: because in this month the Lord thy God brought thee out of Egypt by night.
2 Ku miƙa’yar dabba daga cikin garkenku na tumaki, ko na shanu a matsayin Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji zai zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa.
And thou shalt sacrifice the phase to the Lord thy God, of sheep, and of oxen, in the place which the Lord thy God shall choose, that his name may dwell there.
3 Kada ku ci shi da burodin da aka yi da yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, burodi ne na wahala, gama kun bar Masar da gaggawa, saboda haka dukan kwanakin rayuwarku za ku tuna da lokacin da kuka fita daga Masar.
Thou shalt not eat with it leavened bread: seven days shalt thou eat without leaven, the bread of affliction, because thou camest out of Egypt in fear: that thou mayst remember the day of thy coming out of Egypt, all the days of thy life.
4 Kada a iske yisti a cikin mallakarku a dukan ƙasarku har kwana bakwai. Kada ku bar wani nama na hadayar da kuka yi a yammancin ranar farko, yă kwana har safe.
No leaven shall be seen in all thy coasts for seven days, neither shall any of the flesh of that which was sacrificed the first day in the evening remain until morning.
5 Kada ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa a wani garin da Ubangiji Allahnku yake ba ku,
Thou mayst not immolate the phase in any one of thy cities, which the Lord thy God will give thee:
6 sai dai a wurin da ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa. A can za ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa da yamma, sa’ad da rana tana fāɗuwa, a ranar tunawa da fitowarku daga Masar.
But in the place which the Lord thy God shall choose, that his name may dwell there: thou shalt immolate the phase in the evening, at the going down of the sun, at which time thou camest out of Egypt.
7 Ku gasa shi, ku kuma ci a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa. Sa’an nan da safe, ku dawo cikin tentunanku.
And thou shalt dress, and eat it in the place which the Lord thy God shall choose, and in the morning rising up thou shalt go into thy dwellings.
8 Kwana shida za ku ci burodi marar yisti, a rana ta bakwai kuma sai ku yi taro ga Ubangiji Allahnku, a cikin wannan rana ba za ku yi kowane irin aiki ba.
Six days shalt thou eat unleavened bread: and on the seventh day, because it is the assembly of the Lord thy God, thou shalt do no work.
9 Ku ƙirga makoni bakwai, wato, ku fara ƙirga mako bakwai ɗin daga lokacin da kuka sa lauje don ku yanke hatsinku da suke tsaye.
Thou shalt number unto thee seven weeks from that day, wherein thou didst put the sickle to the corn.
10 Sa’an nan ku yi shagalin Bikin Makoni ga Ubangiji Allahnku, ta wurin ba da hadaya ta yardar rai daidai da albarkun da Ubangiji Allahnku ya yi muku.
And thou shalt celebrate the festival of weeks to the Lord thy God, a voluntary oblation of thy hand, which thou shalt offer according to the blessing of the Lord thy God.
11 Ku kuma yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawan cikin biranenku, har ma da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikinku.
And thou shalt feast before the Lord thy God, thou, and thy son, and thy daughter, and thy manservant, and thy maidservant, and the Levite that is within thy gates, and the stranger and the fatherless, and the widow, who abide with you: in the place which the Lord thy God shall choose, that his name may dwell there:
12 Ku tuna fa, dā ku bayi ne a Masar, sai ku lura, ku bi waɗannan ƙa’idodi.
And thou shalt remember that thou wast a servant in Egypt: and thou shalt keep and do the things that are commanded.
13 Ku yi shagalin Bikin Tabanakul har kwana bakwai, bayan kuka gama tattara amfanin gona daga masussukarku da kuma daga wuraren matsin inabinku.
Thou shalt celebrate the solemnity also of tabernacles seven days, when thou hast gathered in thy fruit of the barnfloor and of the winepress.
14 Ku yi farin ciki a Bikinku, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawa, da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikin biranenku.
And thou shalt make merry in thy festival time, thou, thy son, and thy daughter, thy manservant, and thy maidservant, the Levite also and the stranger, and the fatherless and the widow that are within thy gates.
15 Kwana bakwai za ku yi shagalin Bikin ga Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa. Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan girbinku da kuma cikin dukan aikin hannuwanku, farin cikinku kuwa zai cika.
Seven days shalt thou celebrate feasts to the Lord thy God in the place which the Lord shall choose: and the Lord thy God will bless thee in all thy fruits, and in every work of thy hands, and thou shalt be in joy.
16 Sau uku a shekara dukan maza su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa; a Bikin Burodi Marar Yisti, da a Bikin Makoni, da kuma a Bikin Tabanakul. Babu wani da zai bayyana a gaban Ubangiji hannu wofi.
Three times in a year shall all thy males appear before the Lord thy God in the place which he shall choose: in the feast of unleavened bread, in the feast of weeks, and in the feast of tabernacles. No one shall appear with his hands empty before the Lord:
17 Dole kowannenku yă kawo kyauta daidai yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace shi.
But every one shall offer according to what he hath, according to the blessing of the Lord his God, which he shall give him.
18 Ku naɗa alƙalai da shugabanni don kowace kabila, a kowane birnin da Ubangiji Allahnku yake ba ku, za su kuma shari’anta mutane ba nuna bambanci.
Thou shalt appoint judges and magistrates in all thy gates, which the Lord thy God shall give thee, in all thy tribes: that they may judge the people with just judgment,
19 Kada ku ɓata shari’a, ko ku nuna bambanci. Kada ku karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta idanu mai hikima, yă murɗe maganar mai gaskiya.
And not go aside to either part. Thou shalt not accept person nor gifts: for gifts blind the eyes of the wise, and change the words of the just.
20 Gaskiya ce kaɗai za ku bi don ku rayu, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Thou shalt follow justly after that which is just: that thou mayst live and possess the land, which the Lord thy God shall give thee.
21 Kada ku kafa wani ginshiƙin itacen Ashera kusa da bagaden da kuka gina wa Ubangiji Allahnku,
Thou shalt plant no grove, nor any tree near the altar of the Lord thy God:
22 kada kuma ku tayar da dutse mai tsarki, gama waɗannan ne Ubangiji Allahnku yana ƙi.
Neither shalt thou make nor set up to thyself a statue: which things the Lord thy God hateth.