< Maimaitawar Shari’a 16 >

1 Ku kiyaye watan Abib, ku kuma yi shagalin Bikin Ƙetarewar Ubangiji Allahnku, domin a watan Abib ne ya fitar da ku daga Masar da dad dare.
Observe the month of Abib, and keep the Passover to Jehovah thy God, for in the month of Abib Jehovah thy God brought thee forth out of Egypt by night.
2 Ku miƙa’yar dabba daga cikin garkenku na tumaki, ko na shanu a matsayin Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji zai zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa.
And thou shall sacrifice the Passover to Jehovah thy God, of the flock and the herd, in the place which Jehovah shall choose to cause his name to dwell there.
3 Kada ku ci shi da burodin da aka yi da yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, burodi ne na wahala, gama kun bar Masar da gaggawa, saboda haka dukan kwanakin rayuwarku za ku tuna da lokacin da kuka fita daga Masar.
Thou shall eat no leavened bread with it. Seven days thou shall eat unleavened bread with it, even the bread of affliction, for thou came forth out of the land of Egypt in haste, that thou may remember the day when thou came forth out of the land of Egypt all the days of thy life.
4 Kada a iske yisti a cikin mallakarku a dukan ƙasarku har kwana bakwai. Kada ku bar wani nama na hadayar da kuka yi a yammancin ranar farko, yă kwana har safe.
And there shall be no leaven seen with thee in all thy borders seven days. Neither shall any of the flesh, which thou sacrifice the first day at evening, remain all night until the morning.
5 Kada ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa a wani garin da Ubangiji Allahnku yake ba ku,
Thou may not sacrifice the Passover within any of thy gates, which Jehovah thy God gives thee,
6 sai dai a wurin da ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa. A can za ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa da yamma, sa’ad da rana tana fāɗuwa, a ranar tunawa da fitowarku daga Masar.
but at the place which Jehovah thy God shall choose to cause his name to dwell in, there thou shall sacrifice the Passover at evening, at the going down of the sun, at the season that thou came forth out of Egypt.
7 Ku gasa shi, ku kuma ci a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa. Sa’an nan da safe, ku dawo cikin tentunanku.
And thou shall roast and eat it in the place which Jehovah thy God shall choose, and thou shall turn in the morning, and go to thy tents.
8 Kwana shida za ku ci burodi marar yisti, a rana ta bakwai kuma sai ku yi taro ga Ubangiji Allahnku, a cikin wannan rana ba za ku yi kowane irin aiki ba.
Six days thou shall eat unleavened bread, and on the seventh day shall be a solemn assembly to Jehovah thy God. Thou shall do no work.
9 Ku ƙirga makoni bakwai, wato, ku fara ƙirga mako bakwai ɗin daga lokacin da kuka sa lauje don ku yanke hatsinku da suke tsaye.
Thou shall number to thee seven weeks. From the time thou begin to put the sickle to the standing grain thou shall begin to number seven weeks.
10 Sa’an nan ku yi shagalin Bikin Makoni ga Ubangiji Allahnku, ta wurin ba da hadaya ta yardar rai daidai da albarkun da Ubangiji Allahnku ya yi muku.
And thou shall keep the feast of weeks to Jehovah thy God with a tribute of a freewill offering from thy hand, which thou shall give, according as Jehovah thy God blesses thee.
11 Ku kuma yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawan cikin biranenku, har ma da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikinku.
And thou shall rejoice before Jehovah thy God, thou, and thy son, and thy daughter, and thy man-servant, and thy maid-servant, and the Levite who is within thy gates, and the sojourner, and the fatherless, and the widow, who are in the midst of thee, in the place which Jehovah thy God shall choose to cause his name to dwell there,
12 Ku tuna fa, dā ku bayi ne a Masar, sai ku lura, ku bi waɗannan ƙa’idodi.
and thou shall remember that thou were a bondman in Egypt. And thou shall observe and do these statutes.
13 Ku yi shagalin Bikin Tabanakul har kwana bakwai, bayan kuka gama tattara amfanin gona daga masussukarku da kuma daga wuraren matsin inabinku.
Thou shall keep the feast of tabernacles seven days after thou have gathered in from thy threshing-floor and from thy winepress.
14 Ku yi farin ciki a Bikinku, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawa, da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikin biranenku.
And thou shall rejoice in thy feast, thou, and thy son, and thy daughter, and thy man-servant, and thy maid-servant, and the Levite, and the sojourner, and the fatherless, and the widow, who are within thy gates.
15 Kwana bakwai za ku yi shagalin Bikin ga Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa. Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan girbinku da kuma cikin dukan aikin hannuwanku, farin cikinku kuwa zai cika.
Seven days thou shall keep a feast to Jehovah thy God in the place which Jehovah shall choose, because Jehovah thy God will bless thee in all thine increase, and in all the work of thy hands, and thou shall be altogether joyful.
16 Sau uku a shekara dukan maza su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa; a Bikin Burodi Marar Yisti, da a Bikin Makoni, da kuma a Bikin Tabanakul. Babu wani da zai bayyana a gaban Ubangiji hannu wofi.
Three times in a year all thy males shall appear before Jehovah thy God in the place which he shall choose: in the feast of unleavened bread, and in the feast of weeks, and in the feast of tabernacles. And they shall not appear before Jehovah empty.
17 Dole kowannenku yă kawo kyauta daidai yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace shi.
Every man shall give as he is able, according to the blessing of Jehovah thy God which he has given thee.
18 Ku naɗa alƙalai da shugabanni don kowace kabila, a kowane birnin da Ubangiji Allahnku yake ba ku, za su kuma shari’anta mutane ba nuna bambanci.
Thou shall make judges and officers for thee in all thy gates, which Jehovah thy God gives thee, according to thy tribes, and they shall judge the people with righteous judgment.
19 Kada ku ɓata shari’a, ko ku nuna bambanci. Kada ku karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta idanu mai hikima, yă murɗe maganar mai gaskiya.
Thou shall not distort justice. Thou shall not respect persons, neither shall thou take a bribe, for a bribe blinds the eyes of the wise, and perverts the words of the righteous.
20 Gaskiya ce kaɗai za ku bi don ku rayu, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Thou shall follow that which is altogether just, that thou may live, and inherit the land which Jehovah thy God gives thee.
21 Kada ku kafa wani ginshiƙin itacen Ashera kusa da bagaden da kuka gina wa Ubangiji Allahnku,
Thou shall not plant for thee an Asherah of any kind of tree beside the altar of Jehovah thy God, which thou shall make for thee.
22 kada kuma ku tayar da dutse mai tsarki, gama waɗannan ne Ubangiji Allahnku yana ƙi.
Neither shall thou set up a pillar for thee, which Jehovah thy God hates.

< Maimaitawar Shari’a 16 >