< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
De sept en sept ans tu feras l'année de relâche.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
Et voici comment se fera l'année de relâche. Que tout créancier se relâche de son droit sur ce qu'il a prêté à son prochain, qu'il ne presse point son prochain et son frère, quand on aura proclamé l'année de relâche à l'honneur de l'Éternel.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Tu pourras presser l'étranger; mais si tu as affaire avec ton frère, tu lui donneras du relâche,
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Afin qu'il n'y ait point de pauvre chez toi. Car l'Éternel te bénira certainement dans le pays que l'Éternel ton Dieu te donne en héritage pour le posséder,
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
Pourvu seulement que tu obéisses à la voix de l'Éternel ton Dieu, pour prendre garde à pratiquer tous ces commandements que je te prescris aujourd'hui.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
Quand l'Éternel ton Dieu t'aura béni, comme il te l'a dit, tu prêteras sur gage à beaucoup de nations, et tu n'emprunteras point sur gage; tu domineras sur beaucoup de nations, et elles ne domineront point sur toi.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
Quand un de tes frères sera pauvre au milieu de toi, dans l'une de tes portes, dans le pays que l'Éternel ton Dieu te donne, tu n'endurciras point ton cœur, et tu ne resserreras point ta main devant ton frère pauvre.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
Mais tu ne manqueras pas de lui ouvrir ta main, et de lui prêter sur gage ce dont il aura besoin.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Prends garde à toi, qu'il n'y ait une pensée impie dans ton cœur, et que tu ne dises: La septième année, l'année de relâche, approche; et que, ton œil étant sans pitié envers ton frère pauvre pour ne lui rien donner, il ne crie contre toi à l'Éternel, et qu'il n'y ait du péché en toi.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Tu ne manqueras point de lui donner, et ton cœur ne lui donnera point à regret; car, à cause de cela, l'Éternel ton Dieu te bénira dans toutes tes œuvres et dans tout ce à quoi tu mettras la main.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
Car il y aura toujours des pauvres dans le pays; c'est pourquoi je te fais ce commandement, et je te dis: Ne manque point d'ouvrir ta main à ton frère affligé et pauvre dans ton pays.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
Quand ton frère d'entre les Hébreux, homme ou femme, te sera vendu, il te servira six ans, mais à la septième année tu le renverras libre de chez toi.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
Et quand tu le renverras libre de chez toi, tu ne le renverras point à vide;
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Tu ne manqueras point de le charger de quelque chose de ton troupeau, de ton aire, et de ta cuve; tu lui donneras des biens dont l'Éternel ton Dieu t'aura béni.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Et souviens-toi que tu as été esclave au pays d'Égypte, et que l'Éternel ton Dieu t'en a racheté; c'est pour cela que je te commande ceci aujourd'hui.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
Mais s'il arrive qu'il te dise: Je ne sortirai point de chez toi; parce qu'il t'aime, toi et ta maison, parce qu'il se trouve bien avec toi;
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
Alors tu prendras un poinçon, et tu lui perceras l'oreille contre la porte, et il sera ton serviteur à toujours; et tu en feras de même à ta servante.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
Qu'il ne te paraisse point dur de le renvoyer libre de chez toi; car il t'a servi six ans, pour la moitié du salaire d'un mercenaire; et l'Éternel ton Dieu te bénira en tout ce que tu feras.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Tu consacreras à l'Éternel ton Dieu tout premier-né mâle qui naîtra de ton gros et de ton menu bétail. Tu ne laboureras point avec le premier-né de ta vache, et tu ne tondras point le premier-né de tes brebis;
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
Tu le mangeras, toi et ta famille, chaque année, devant l'Éternel ton Dieu, au lieu que l'Éternel aura choisi.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
Mais s'il a quelque défaut, s'il est boiteux ou aveugle, ou s'il a quelque autre mauvais défaut, tu ne le sacrifieras point à l'Éternel ton Dieu,
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Mais tu le mangeras dans tes portes; celui qui est souillé et celui qui est pur en mangeront l'un et l'autre, comme on mange du daim ou du cerf.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Seulement tu n'en mangeras point le sang, tu le répandras sur la terre comme l'eau.

< Maimaitawar Shari’a 15 >