< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
De sept en sept ans tu célébreras [l'année de] relâche.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
Et c'est ici la manière [de célébrer l'année] de relâche. Que tout homme ayant droit d'exiger quelque chose que ce soit, qu'il puisse exiger de son prochain, donnera relâche, et ne l'exigera point de son prochain ni de son frère, quand on aura proclamé le relâche, en l'honneur de l'Eternel.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Tu pourras exiger de l'étranger; mais quand tu auras à faire avec ton frère, tu lui donneras du relâche;
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Afin qu'il n'y ait au milieu de toi aucun pauvre; car l'Eternel te bénira certainement au pays que l'Eternel ton Dieu te donne en héritage pour le posséder.
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
[Pourvu] seulement que tu obéisses à la voix de l'Eternel ton Dieu, et que tu prennes garde à faire ces commandements que je te prescris aujourd'hui.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
Parce que l'Eternel ton Dieu t'aura béni comme il t'en a parlé, tu prêteras sur gages à plusieurs nations, et tu n'emprunteras point sur gages. Tu domineras sur plusieurs nations, et elles ne domineront point sur toi.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
Quand un de tes frères sera pauvre au milieu de toi, en quelque lieu de ta demeure, dans le pays que l'Eternel ton Dieu te donne, tu n'endurciras point ton cœur, et tu ne resserreras point ta main à ton frère, qui sera pauvre.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
Mais tu ne manqueras pas de lui ouvrir ta main, et de lui prêter sur gages, autant qu'il en aura besoin pour son indigence, dans laquelle il se trouvera.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Prends garde à toi, que tu n'aies dans on cœur quelque méchante intention, et [que] tu ne dises: La septième année, qui est l'année de relâche, approche; et que ton œil étant malin contre ton frère pauvre, afin de ne lui rien donner, il ne crie à l'Eternel contre toi, et qu'il n'y ait du péché en toi.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Tu ne manqueras point de lui donner, et ton cœur ne lui donnera point à regret; car à cause de cela l'Eternel ton Dieu te bénira dans toute ton œuvre, et dans tout ce à quoi tu mettras la main.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
Car il ne manquera pas de pauvres au pays; c'est pourquoi je te commande, en disant: Ne manque point d'ouvrir ta main à ton frère, [savoir], à l'affligé, et au pauvre de ton peuple en ton pays.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
Quand quelqu'un d'entre tes frères, soit Hébreu ou Hébreue, te sera vendu, il te servira six ans; mais en la septième année tu le renverras libre de chez toi.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
Et quand tu le renverras libre de chez toi, tu ne le renverras point vide.
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Tu ne manqueras pas de le charger de quelque chose de ton troupeau, de ton aire, et de ta cuve; tu lui donneras de ce en quoi l'Eternel ton Dieu t'aura béni.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Et qu'il te souvienne que tu as été esclave au pays d'Egypte, et que l'Eternel ton Dieu t'en a racheté; et c'est pour cela que je te commande ceci aujourd'hui.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
Mais s'il arrive qu'il te dise: Que je ne sorte point de chez toi; parce qu'il t'aime, toi, et ta maison, et qu'il se trouve bien avec toi;
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
Alors tu prendras une alêne, et tu lui perceras l'oreille contre la porte, et il sera ton serviteur à toujours, tu en feras de même à ta servante.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
Qu'il ne te soit point fâcheux de le renvoyer libre de chez toi, car il t'a servi six ans, qui est le double du salaire du mercenaire; et l'Eternel ton Dieu te bénira en tout ce que tu feras.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Tu sanctifieras à l'Eternel ton Dieu tout premier-né mâle qui naîtra de ton gros ou menu bétail. Tu ne laboureras point avec le premier-né de ta vache; et tu ne tondras point le premier-né de tes brebis.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
Tu le mangeras, toi et ta famille, chaque année en la présence de l'Eternel ton Dieu, au lieu que l'Eternel aura choisi.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
Mais s'il a quelque défaut, [tellement qu'il soit] boiteux ou aveugle, ou qu'il ait quelque autre mauvais défaut, tu ne le sacrifieras point à l'Eternel ton Dieu;
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Mais tu le mangeras au lieu de ta demeure. Celui qui est souillé, et celui qui est net [en mangeront], comme [on mange] du daim, et du cerf.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Seulement tu n'en mangeras point le sang, [mais] tu le répandras sur la terre, comme de l'eau.

< Maimaitawar Shari’a 15 >