< Maimaitawar Shari’a 15 >
1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
At the end of [every] seven years thou shalt make a release.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
And this [is] the manner of the release: Every creditor that lendeth [aught] to his neighbor shall release [it]; he shall not exact [it] of his neighbor, or of his brother; because it is called the LORD'S release.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Of a foreigner thou mayest exact [it again]: but [that] which is thine with thy brother thy hand shall release:
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Save when there shall be no poor among you; for the LORD shall greatly bless thee in the land which the LORD thy God giveth thee [for] an inheritance to possess it:
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
Only if thou shalt carefully hearken to the voice of the LORD thy God, to observe to do all these commandments which I command thee this day.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
For the LORD thy God shall bless thee, as he promised thee: and thou shalt lend to many nations, but thou shalt not borrow; and thou shalt reign over many nations, but they shall not reign over thee.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
If there shall be among you a poor man of one of thy brethren within any of thy gates in thy land which the LORD the God giveth thee, thou shalt not harden thy heart, nor shut thy hand from thy poor brother:
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
But thou shalt open thy hand wide to him, and shalt surely lend him sufficient for his need, [in that] which he wanteth.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Beware that there be not a thought in thy wicked heart, saying, The seventh year, the year of release, is at hand; and thy eye shall be evil against thy poor brother, and thou shalt give him naught; and he shall cry to the LORD against thee, and it shall be sin to thee.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Thou shalt surely give him, and thy heart shall not be grieved when thou givest to him: because that for this thing the LORD thy God shall bless thee in all thy works, and in all that thou puttest thy hand to.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
For the poor shall never cease from the land: therefore I command thee, saying, Thou shalt open thy hand wide to thy brother, to thy poor, and to thy needy, in thy land.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
[And] if thy brother, a Hebrew man, or a Hebrew woman, shall be sold to thee, and serve thee six years; then in the seventh year thou shalt let him go free from thee.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
And when thou sendest him out free from thee, thou shalt not let him depart empty:
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Thou shalt furnish him liberally out of thy flock, and out of thy floor, and out of thy wine-press: [of that] with which the LORD thy God hath blessed thee thou shalt give to him.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
And thou shalt remember that thou wast a bond-man in the land of Egypt, and the LORD thy God redeemed thee: therefore I command thee this thing this day.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
And it shall be, if he shall say to thee, I will not leave thee; because he loveth thee and thy house, because he is well with thee;
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
Then thou shalt take an awl, and thrust [it] through his ear into the door, and he shall be thy servant for ever. And also to thy maid-servant thou shalt do likewise.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
It shall not seem hard to thee, when thou sendest him away free from thee; for he hath been of double the worth of a hired servant [to thee], in serving thee six years: and the LORD thy God shall bless thee in all that thou doest.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
All the firstling males that come of thy herd and of thy flock thou shalt sanctify to the LORD thy God: thou shalt do no work with the firstling of thy bullock, nor shear the firstling of thy sheep.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
Thou shalt eat [it] before the LORD thy God year by year in the place which the LORD shall choose, thou and thy household.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
And if there is [any] blemish in it, [as if it is] lame, or blind, [or hath] any ill blemish, thou shalt not sacrifice it to the LORD thy God.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Thou shalt eat it within thy gates: the unclean and the clean [person shall eat it] alike, as the roebuck, and as the hart.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Only thou shalt not eat its blood; thou shalt pour it upon the ground as water.