< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
“At the end of every seven years, you must (cancel all debts/tell people who owe you money that they do not need to pay it back).
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
Do it like this: Each of you who has lent money to a fellow Israeli must cancel that debt. You must not insist that he pay it back. You must do that because Yahweh has declared that the debts must be canceled [every seven years].
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
[During that year] you may require foreigners [who live among you] to pay what they owe you, but you must not try to require that any fellow Israeli pay you what he owes you.
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Yahweh our God will bless you in the land that he is giving to you. If you obey Yahweh our God and obey all the commandments that I am giving to you today, there will not be any poor people among you.
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
Yahweh our God will bless you like he has promised to do, and you will [be able to] lend money to people of other people-groups, but you will not [need to] borrow from any of them. You will control [the finances of] many people-groups, but they will not control your [finances].
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
“In the towns that Yahweh our God is giving to you, if there are any Israelis who are poor, do not be selfish [IDM] and refuse [IDM] to help them.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
Instead, be generous [IDM] and lend to them the money that they need.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Be sure that you do not say to yourself, ‘The year when debts will be canceled is near, [so I do not want to lend anyone any money now, because he will not need to pay it back when that year comes].’ It would be evil to even think that. If you act in an unfriendly way toward a needy fellow Israeli, and give him nothing, he will cry out to Yahweh about you, and [Yahweh will say that] you have sinned [by not helping that person].
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Give freely to poor people and give generously [IDM].
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
If you do that, Yahweh will bless you in everything that you do. There will always be some poor people in your land, so I command you to give generously to poor [DOU] people.”
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
“If any of your fellow Israeli men or women sell themselves to one of you [to become your slave], you must free them after they have worked for you for six years. When the seventh year comes, you must free them.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
When you free them, do not allow them to go (empty-handed/without giving them anything).
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Give to them generously from the things with which Yahweh has blessed you—sheep, grain, and wine.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Do not forget that your ancestors were once slaves in Egypt, and Yahweh our God freed them. That is the reason that I am now commanding you to do this.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
“But one of your slaves may say, ‘I do not want to leave you.’ He loves you and your family, because you have treated him well.
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
If he says that, take him to the door of your house and, [while he stands against the doorway], pierce one of his earlobes with (an awl/a sharp pointed tool). That will indicate that he will be your slave for the rest of his life. Do the same thing to any female slave [who does not want to leave you].
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
“Do not complain when you are required to free your slaves. [Keep in mind that] they served you for six years, and you paid them only half as much as you pay the servants that you hire. [If you free them, ] Yahweh our God will bless you in everything that you do.”
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
“(Set aside for/Dedicate to) Yahweh our God the firstborn male animals from your cattle and sheep. Do not force them to do any work for you, and do not (shear/cut off) the wool [of the firstborn animals to sell the wool].
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
You and your family may [kill them and] eat their meat in the presence of Yahweh at the place that Yahweh chooses [for you to worship him].
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
But if the animals have any defects, if they are lame or blind, or if they have any other serious defect, you must not sacrifice them to Yahweh our God.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
You may [kill and] eat [the meat of those animals] at your homes. Those who have done things that cause them to become unacceptable to God and those who have not done such things are permitted to eat that meat, just like anyone is permitted to eat the meat of a deer or an antelope.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
But you must not eat any of the blood; you must drain all the blood on the ground [when you kill those animals].”

< Maimaitawar Shari’a 15 >