< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
Every seven years you shall make a release.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
And this [is] the ordinance of the release: you shall remit every private debt which your neighbor owes you, and you shall not ask payment of it from your brother; for it has been called a release to the Lord your God.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Of a stranger you shall ask again whatever he has of your, but to your brother you shall remit his debt to you.
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
For [thus] there shall not be a poor person in the midst of you, for the Lord your God will surely bless you in the land which the Lord your God gives you by inheritance, that you should inherit it.
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
And if you shall indeed listen to the voice of the Lord your God, to keep and do all these commandments, as many as I charge you this day,
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
(for the Lord your God has blessed you in the way of which he spoke to you, ) then you shall lend to many nations, but you shall not borrow; and you shall rule over many nations, but they shall not rule over you.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
And if there shall be in the midst of you a poor [man] of your brethren in one of your cities in the land, which the Lord your God gives you, you shall not harden your heart, neither shall you by any means close up your hand from your brother who is in lack.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
You shall surely open your hands to him, and shall lend to him as much as he wants according to his need.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Take heed to yourself that there be not a secret thing in your heart, an iniquity, saying, The seventh year, the year of release, draws near; and your eye shall be evil to your brother that is in lack, and you shall not give to him, and he shall cry against you to the Lord, and there shall be great sin in you.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
You shall surely give to him, and you shall lend him as much as he wants, according as he is in need; and you shall not grudge in your heart as you give to him, because on this account the Lord your God will bless you in all your works, and in all things on which you shall lay your hand.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
For the poor shall not fail off your land, therefore I charge you to do this thing, saying, You shall surely open your hands to your poor brother, and to him that is distressed upon your land.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
And if your brother [or sister], a Hebrew man or a Hebrew woman, be sold to you, he shall serve you six years, and in the seventh year you shall send him out free from you.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
And when you shall send him out free from you, you shall not send him out empty.
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
You shall give him provision for the way from your flock, and from your corn, and from your wine; as the Lord your God has blessed you, you shall give to him.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
And you shall remember that you were a servant in the land of Egypt, and the Lord your God redeemed you from thence; therefore I charge you to do this thing.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
And if he should say to you, I will not go out from you, because he continues to love you and your house, because he is well with you;
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
then you shall take an awl, and bore his ear through to the door, and he shall be your servant for ever; and in like manner shall you do to your maidservant.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
It shall not seem hard to you when they are sent out free from you, because [your servant] has served you six years according to the annual hire of a hireling; so the Lord your God shall bless you in all things whatever you may do.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Every firstborn that shall be born among your kine and your sheep, you shall sanctify the males to the Lord your God; you shall not work with your firstborn calf, and you shall not shear the firstborn of your sheep.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
You shall eat it before the Lord year by year in the place which the Lord your God shall choose, you and your house.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
And if there be in it a blemish, if it be lame or blind, an evil blemish, you shall not sacrifice it to the Lord your God.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
You shall eat it in your cities; the unclean in you and the clean shall eat it in like manner, as the doe or the stag.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Only you shall not eat the blood; you shall pour it out on the earth as water.

< Maimaitawar Shari’a 15 >