< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
“In the seventh year, you shall perform a remission,
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
which shall be celebrated according to this order. Anyone to whom anything is owed, by his friend or neighbor or brother, will not be able to request its return, because it is the year of remission of the Lord.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
From the sojourner and the new arrival, you may require its return. From your fellow countryman and neighbor, you will not have the power to request its return.
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
And there shall not be anyone indigent or begging among you, so that the Lord your God may bless you in the land which he will deliver to you as a possession.
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
But only if you heed the voice of the Lord your God, and keep to all that he has ordered, that which I am entrusting to you this day, will he bless you, just as he has promised.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
You shall lend money to many nations, and you yourselves shall borrow in return from no one. You shall rule over very many nations, and no one shall rule over you.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
If one of your brothers, who dwells within the gates of your city, in the land which the Lord your God will give to you, falls into poverty, you shall not harden your heart, nor tighten your hand.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
Instead, you shall open your hand to the poor, and you shall lend to him whatever you perceive him to need.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Take care, lest perhaps an impious thought might creep within you, and you might say in your heart: ‘The seventh year of remission approaches.’ And so you might turn your eyes away from your poor brother, unwilling to lend to him what he has asked. If so, then he may cry out against you to the Lord, and it will be a sin for you.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Instead, you shall give to him. Neither shall you do anything craftily while assisting him in his needs, so that the Lord your God may bless you, at all times and in all things to which you will put your hand.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
The poor will not be absent from the land of your habitation. For this reason, I instruct you to open your hand to your indigent and poor brother, who lives among you in the land.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
When your brother, a Hebrew man or a Hebrew woman, has been sold to you, and has served you for six years, in the seventh year you shall set him free.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
And when you grant his freedom, you shall by no means permit him to go away empty.
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Instead, you shall give to him, for his journey, from your flocks and threshing floor and winepress, with which the Lord your God has blessed you.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Remember that you yourself also served in the land of Egypt, and the Lord your God set you free. And therefore, I now command this of you.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
But if he will say, ‘I am not willing to depart,’ because he loves you and your household, and because he feels that it would be good for him to stay with you,
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
then you shall take an awl and pierce his ear, at the door of your house. And he shall serve you even forever. You shall also act similarly toward your woman servant.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
You should not avert your eyes from them when you set them free, because he has served you for six years, in a manner deserving of the pay of a hired hand. So may the Lord your God bless you in all the works that you do.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Of the firstborn, those born from your herds and sheep, you shall sanctify to the Lord your God whatever is of the male sex. You shall not put the firstborn of the oxen to work, nor shall you shear the firstborn of the sheep.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
In the sight of the Lord your God, you shall eat these, each year, in the place which the Lord will choose, you and your household.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
But if it has a blemish, or is lame, or is blind, or if it is in any part deformed or debilitated, it shall not be immolated to the Lord your God.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Instead, you shall eat it within the gates of your city. The clean as well as the unclean alike shall feed on these, such as the roe deer and the stag.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
This alone shall you observe: that you do not eat their blood, but pour it upon the ground like water.”

< Maimaitawar Shari’a 15 >