< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
At the end of every seven years thou shalt make a release.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
And this is the manner of the release: every creditor shall release that which he hath lent unto his neighbor; he shall not exact it of his neighbor and his brother; because Jehovah’s release hath been proclaimed.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Of a foreigner thou mayest exact it: but whatsoever of thine is with thy brother thy hand shall release.
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Howbeit there shall be no poor with thee (for Jehovah will surely bless thee in the land which Jehovah thy God giveth thee for an inheritance to possess it),
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
if only thou diligently hearken unto the voice of Jehovah thy God, to observe to do all this commandment which I command thee this day.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
For Jehovah thy God will bless thee, as he promised thee: and thou shalt lend unto many nations, but thou shalt not borrow; and thou shalt rule over many nations, but they shall not rule over thee.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
If there be with thee a poor man, one of thy brethren, within any of thy gates in thy land which Jehovah thy God giveth thee, thou shalt not harden thy heart, nor shut thy hand from thy poor brother;
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
but thou shalt surely open thy hand unto him, and shalt surely lend him sufficient for his need [in that] which he wanteth.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Beware that there be not a base thought in thy heart, saying, The seventh year, the year of release, is at hand; and thine eye be evil against thy poor brother, and thou give him nought; and he cry unto Jehovah against thee, and it be sin unto thee.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Thou shalt surely give him, and thy heart shall not be grieved when thou givest unto him; because that for this thing Jehovah thy God will bless thee in all thy work, and in all that thou puttest thy hand unto.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
For the poor will never cease out of the land: therefore I command thee, saying, Thou shalt surely open thy hand unto thy brother, to thy needy, and to thy poor, in thy land.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
If thy brother, a Hebrew man, or a Hebrew woman, be sold unto thee, and serve thee six years; then in the seventh year thou shalt let him go free from thee.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
And when thou lettest him go free from thee, thou shalt not let him go empty:
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
thou shalt furnish him liberally out of thy flock, and out of thy threshing-floor, and out of thy winepress; as Jehovah thy God hath blessed thee thou shalt give unto him.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
And thou shalt remember that thou wast a bondman in the land of Egypt, and Jehovah thy God redeemed thee: therefore I command thee this thing to-day.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
And it shall be, if he say unto thee, I will not go out from thee; because he loveth thee and thy house, because he is well with thee;
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
then thou shalt take an awl, and thrust it through his ear unto the door, and he shall be thy servant for ever. And also unto thy maid-servant thou shalt do likewise.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
It shall not seem hard unto thee, when thou lettest him go free from thee; for to the double of the hire of a hireling hath he served thee six years: and Jehovah thy God will bless thee in all that thou doest.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
All the firstling males that are born of thy herd and of thy flock thou shalt sanctify unto Jehovah thy God: thou shalt do no work with the firstling of thy herd, nor shear the firstling of thy flock.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
Thou shalt eat it before Jehovah thy God year by year in the place which Jehovah shall choose, thou and thy household.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
And if it have any blemish, [as if it be] lame or blind, any ill blemish whatsoever, thou shalt not sacrifice it unto Jehovah thy God.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Thou shalt eat it within thy gates: the unclean and the clean [shall eat it] alike, as the gazelle, and as the hart.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Only thou shalt not eat the blood thereof; thou shalt pour it out upon the ground as water.

< Maimaitawar Shari’a 15 >