< Maimaitawar Shari’a 15 >
1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
E giko mar higa mar abiriyo gope duto nyaka we.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
Ma e kaka onego time: Ngʼato ka ngʼato nyaka we gope ma ja-Israel wadgi nigo. Ok onego okaw chudo kuom ja-Israel kata wadgi nikech ndalo mar weyo gowi e nyim Jehova Nyasaye oselandi.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Jopinje mamoko to unyalo nyiso mondo ochulu gope ma gin-go, to gowi moro amora ma ja-Israel wadu nigo to nyaka iwene.
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
Kata kamano, ngʼat modhier ok onego bedi e dieru, nikech piny ma Jehova Nyasaye ma Nyasachu miyou kod jou mondo ukaw kaka girkeni obiro gwedho,
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
mana ka urito chike duto mag Jehova Nyasaye ma Nyasachu, kendo urito buchene duto ma amiyou kawuono.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
Kuom mano Jehova Nyasaye ma Nyasachu biro gwedhou kaka osewacho, kendo ubiro olo ogendini mangʼeny mwandu to un ok unuol kuomgi. Ubiro bedo gi loch kuom pinje mamoko to un onge manobed kod loch kuomu.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
Ka nitie jachan e kind owete moa e mier mag piny ma Jehova Nyasaye nomiu, to kik ubed gi chuny mapek kata lep ma wuoyo marach ewi owadu modhierno.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
To beduru mangʼwon kendo uholgi gimoro amora magidwaro.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Kata bedni higa mar abiriyo chiegni chopo to kik ubed gi ich lit mutamru olo owadu man-gi dwaro. Ka mano otimore, to owaduno nyalo mako bura e nyim Jehova Nyasaye mi ubed joketho.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Chiwreuru gi chuny man thuolo, to ka utimo kamano to Jehova Nyasaye ma Nyasachu biro gwedho tijeu duto kod gimoro amora ma udwaro timo.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
Joma ochando nobedie e pinyu ndalo duto. Kuom mano achikou mondo ubed gi chuny ma thuolo kuom oweteu, joma odhier kod joma ochando e pinyu.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
Ka ja-Hibrania wadu madichwo kata madhako ochiwore mondo ingʼiewe kendo otini kuom higni auchiel, to e higa mar abiriyo nyaka iweye obed thuolo.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
Kendo ka iweye mondo odhi ka en thuolo, to kik igole odhi gi lwete nono.
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Kowe mabup gi chuny ma thuolo kimiye jamni, kar dino cham kod divai. Bedne mangʼwon kendo imiye kaluwore gi kaka Jehova Nyasaye ma Nyasachi osegwedhi.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Paruru nine un wasumbini e piny Misri to Jehova Nyasaye ma Nyasachu noresou. Mano emomiyo amiyou chikni kawuono.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
Ka jatichni owacho niya, “Ok adwar weyi,” nikech oheri kod jo-dalani duto kendo owinjo maber ka odak kodu,
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
to kaw riwi kendo ituchgo ite kiteno e dhoot mondo koro obed misumbani nyaka chiengʼ tim kamano bende nyaka ne jatichni madhako.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
Kik bedni matek weyo misumbani thuolo nimar higni auchiel mosebedo oromo chudo nyadiriyo maromre kod ngʼatno ma biro tiyoni ndalo. Kitimo kamano to Jehova Nyasaye ma Nyasachi nogwedh gik moko duto mitimo.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Keturu tenge ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu jamni duto machwo mokwong nywolo e kweth jambu. Kik uket rwedhi ma dhou okwongo nywolo e jok bende kik ungʼad yie rombu mokwong nywolo.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
E higa ka higa in kod joodi onego uchamgi e nyim Jehova Nyasaye ma Nyasachu kama en owuon noyier.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
Ka chiayo moro nigi songa, ongʼol kata en muofu kata ka en gi mbala moro amora to ok onego utim kode misango ne Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Onego uchame e miechu uwuon. Joma ok ler gi jomaler nyalo chame mana kaka gichamo mwanda kata nyakech.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Kik ucham remo, to pukgiuru piny mana ka pi.