< Maimaitawar Shari’a 15 >

1 A ƙarshen kowace shekara ta bakwai, dole ku yafe basusuwan da kuke bi.
Naar syv Aar ere til Ende, skal du lade Henstand ske.
2 Ga yadda za ku yafe basusuwan, kowane mai bin bashi, yă yafe bashin da yake bin ɗan’uwansa mutumin Isra’ila. Ba zai bukaci mutumin Isra’ila wanda yake ɗan’uwa yă biya shi bashi ba, gama an yi shelar lokacin da Ubangiji ya ajiye na yafe bashi.
Og saaledes skal der forholdes med denne Henstand: Hver Ejermand, som har laant noget ud af sin Haand, skal give Henstand med det, som han har laant ud til sin Næste; han skal ikke kræve sin Næste eller sin Broder, naar man har udraabt Henstand for Herren.
3 Za ku iya nemi baƙo yă biya ku bashin da kuke binsa, amma dole ku yafe duk wani bashin da kuke bin ɗan’uwa.
Den fremmede maa du kræve; men det, som du har hos din Broder, skal din Haand give Henstand med;
4 Amma bai kamata a sami matalauci a cikinku ba, gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a ƙasar da yake ba ku, ku mallaka a matsayin gādo,
kun at ingen skal blive en Tigger iblandt eder; thi Herren skal meget velsigne dig i det Land, som Herren din Gud giver dig til Arv at eje det;
5 in dai kun yi cikakken biyayya ga Ubangiji Allahnku, kuka kuma lura, kuna kiyaye dukan waɗannan umarnan da nake ba ku yau.
dersom du ikkun hører Herren din Guds Røst, saa at du tager Vare paa at gøre efter alle disse Bud som jeg byder dig i Dag.
6 Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku kamar yadda ya yi alkawari, za ku kuma ba al’ummai masu yawa bashi, amma ba za ku karɓa bashi daga wurin wani ba. Za ku yi mulkin al’ummai masu yawa, babu wata kuwa da za tă yi mulkinku.
Thi Herren din Gud har velsignet dig, som han har tilsagt dig; og du skal laane til mange Folk; men du skal ikke tage til Laans; og du skal herske over mange Folk, men de skulle ikke herske over dig.
7 In akwai matalauci a cikin’yan’uwanku, a duk wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku taurara zuciya, ko ku ƙi saki hannu ga ɗan’uwanku matalauci.
Naar der vorder en fattig iblandt eder, en af dine Brødre, i en af dine Stæder i dit Land, som Herren din Gud giver dig: Da skal du ikke gøre dit Hjerte haardt og ikke lukke din Haand for din fattige Broder.
8 A maimakon haka ku bayar hannu sake, ku kuma ba shi bashi gwargwadon abin da yake bukata a sauƙaƙe.
Men du skal oplade din Haand for ham, og du skal laane ham det, som er nok for hans Mangel, det som ham fattes.
9 Ku yi hankali kada ku riƙe wannan mugun tunani cewa, “Shekara ta bakwai, shekarar yafewar basusuwa, ta yi kusa,” har ku nuna mugun nufi ga ɗan’uwa mabukaci, ku ƙi ba shi wani abu. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.
Tag dig i Vare, at der ikke er en nedrig Tanke i dit Hjerte, at du siger: Det syvende Aar, Henstandsaaret, er nær, og at du er karrig imod din fattige Broder og ikke giver ham, og at han raaber over dig til Herren, og det skal være dig til Synd.
10 Ku bayar hannu sake gare shi, ku kuma yi haka ba tare da gunaguni ba; saboda wannan fa Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan aikinku, da kuma kome da kuka sa hannunku a kai.
Du skal give ham og ikke lade dit Hjerte fortryde det, at du giver ham; thi Herren din Gud skal for denne Sags Skyld velsigne dig i alle dine Gerninger og i alt det, som du udrækker din Haand til.
11 Kullum za ku kasance da matalauta a ƙasar. Saboda haka na umarce ku ku bayar hannu sake ga’yan’uwa da kuma matalauta, da masu bukata a ƙasarku.
Thi fattige ville ikke ophøre at være i Landet; derfor byder jeg dig og siger, at du skal oplade din Haand for din Broder, for den, som trænger hos dig, og for din fattige i dit Land.
12 In ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa, namiji ko ta mace, ya sayar da kansa gare ka, ya kuma bauta maka shekaru shida, a shekara ta bakwai dole ka’yantar da shi.
Naar din Broder, en Hebræer eller en Hebræerinde, sælges til dig, da skal han tjene dig i seks Aar, og i det syvende Aar skal du lade ham fri fra dig.
13 Sa’ad da kuka sake shi, kada ku bar shi yă tafi hannu wofi.
Og naar du lader ham fri fra dig, da skal du ikke lade ham gaa tomhændet.
14 Ku ba shi kyautai hannu sake daga tumakinku, daga masussukarku, da kuma daga wurin matsewar inabinku. Ku ba shi yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace ku.
Du skal rigeligen begave ham af dit smaa Kvæg og af din Lade og af din Perse; det som Herren din Gud velsigner dig med, deraf skal du give ham.
15 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuma ya fisshe ku. Shi ya sa nake ba ku wannan umarni a yau.
Og du skal komme i Hu, at du var en Træl i Ægyptens Land, og at Herren din Gud udløste dig; derfor byder jeg dig dette Ord i Dag.
16 Amma in bawanka ya ce maka, “Ba na so in bar ka,” saboda yana ƙaunarka da iyalinka, ya kuma fiye masa yă zauna da kai,
Og det skal ske, om han siger til dig: Jeg vil ikke gaa ud fra dig, fordi han elsker dig og dit Hus, fordi han lider vel hos dig:
17 sai ka ɗauki basilla ka huda kunnensa a bakin ƙofa, zai kuwa zama bawanka dukan rayuwarsa. Ka yi haka ma wa baiwarka.
Da skal du tage en Syl og stikke i hans Øre og i Døren, saa skal han være dig en Træl bestandig; og saaledes skal du og gøre ved din Tjenestepige.
18 Sa’ad da kuka’yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai albarkace ku a kome da kuke yi.
Lad det ikke være for svart for dine Øjne, at du lader ham fri fra dig; thi han har tjent dig dobbelt, efter en Daglønners Løn, seks Aar; og Herren din Gud skal velsigne dig i alt det, du skal gøre.
19 Ku keɓe wa Ubangiji Allahnku kowane ɗan fari na garkenku na shanu, da na tumaki. Kada ku sa ɗan fari na shanunku aiki, kada kuma ku aske gashin ɗan fari na tumakinku.
Alt det førstefødte, som fødes af dit store Kvæg og af dit smaa Kvæg, naar det er en Han, skal du hellige for Herren din Gud; du skal ikke arbejde med din Okses førstefødte og ikke klippe dine Faars førstefødte.
20 Kowace shekara, kai da iyalinka za ku ci su a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa.
Du skal æde det hvert Aar for Herren din Guds Ansigt paa det Sted, som Herren skal udvælge, du og dit Hus.
21 In dabbar tana da lahani, gurguntaka ko makantaka, ko kuwa tana da wani mugun lahani, kada ku miƙa ta ga Ubangiji Allahnku.
Dog, om der er Lyde paa det, saa det er lamt eller blindt, hvad som helst slem Lyde det er, da skal du ikke ofre det for Herren, din Gud.
22 Sai ku ci a cikin biranenku. Mutum marar tsabta da mai tsabta zai iya ci kamar yadda ake yi da barewa ko mariri.
Inden dine Porte skal du æde det, saavel den urene som den rene, som var det en Raa og en Hjort.
23 Amma kada fa ku ci jinin, ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa.
Dog skal du ikke æde Blodet deraf; du skal udøse det paa Jorden som Vand.

< Maimaitawar Shari’a 15 >