< Maimaitawar Shari’a 14 >

1 Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
I ären Herrans edars Guds barn; skärer eder icke, och görer eder icke skallota öfver edart änne för någon dödan.
2 gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
Ty du äst ett heligt folk Herranom dinom Gud, och Herren hafver utvalt dig, att du skall vara hans eget, utaf all folk som på jordene äro.
3 Kada ku ci wani haramtaccen abu.
Du skall ingen styggelse äta.
4 Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
Men desse äro de djur, som I äta skolen: Fä, får, get, hjort,
5 mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
Rå, buffel, stenbock, enhörning, urnöt, och elgen.
6 Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
Och all djur, som tveklöfvad äro, och idisla, skolen I äta.
7 Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
Men det skolen I icke äta, som idislar, och icke tveklöfvadt är: camelen, haran, cunilen. De som idisla, och icke tveklöfvad äro, de skola vara eder oren.
8 Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
Svinet, ändock det tveklöfvadt är, så idislar det dock icke, det skall vara eder orent; af dess kött skolen I icke äta, och vid dess as skolen I icke komma.
9 Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
Detta är det I äta skolen, utaf allt det i vattnet är: allt det som spol och fjäll hafver, det skolen I äta;
10 Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
Men det som intet spol eller fjäll hafver, det skolen I icke äta; ty det är eder orent.
11 Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
Alla rena foglar äter.
12 Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
Desse af dem äro de som I icke äta skolen: örnen, höken, falken,
13 duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
Fiskagjusen, gladan, gamen med sine art,
14 kowane irin hankaka,
Och alla korpar med deras art,
15 jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
Strutsfoglen, ugglan, göken, sparfhöken med sine art,
16 da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
Stenugglan, ufven, flädermusen,
17 kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
Rördrommen, storken, svanen,
18 zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
Hägren, skrikan med sine art, vidhöfden, och svalan.
19 Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
Och alle foglar, som krypa, skola vara eder orene, och I skolen icke äta dem.
20 Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
De rena foglar skolen I äta.
21 Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
I skolen intet as äta. Främlingenom, som i dinom porte är, må du gifva det, att han det äter, eller sälj det enom främmande; ty du äst ett heligt folk Herranom dinom Gud. Du skall icke koka kidet, medan det ännu dir sina moder.
22 Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
Du skall all år afskilja tionden af allo dine säds frukt, som utaf dinom åker kommer;
23 Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
Och skall äta den för Herranom dinom Gud, på det rum som han utväljer, att hans Namn der bo skall; nämliga af tionden utaf din säd, dino vine, dine oljo, och förstfödningen af ditt fä och din får; på det du skall lära frukta Herran din Gud i alla dina lifsdagar.
24 Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
Om vägen är dig för lång, att du icke kan komma det dit, derföre att det rummet är dig för långt ifrå, som Herren din Gud utvalt hafver, att han vill låta sitt Namn bo der; ty Herren din Gud hafver välsignat dig;
25 to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
Så sälj det allt för penningar, och tag penningarna i dina hand, och gack till det rum, som Herren din Gud utvalt hafver;
26 Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
Och köp för penningarna allt det din själ lyster, vare sig fä, får, vin, stark dryck, eller allt det din själ begärar; och ät det der för Herranom dinom Gud, och var glad, du och ditt hus.
27 Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
Och Leviten, som i dina portar är, honom skall du icke förlåta; förty han hafver ingen lott eller arf med dig.
28 A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
Efter tre år skall du afsöndra all tiond af dine säd i det året, och skall lägga henne i dina portar.
29 saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.
Så skall Leviten komma, som ingen lott eller arf hafver med dig; och främlingen, och den faderlöse, och enkan, som i dina portar äro, och äta, och mätta sig; på det Herren din Gud dig välsigna skall i alla dina händers gerningar, som du gör.

< Maimaitawar Shari’a 14 >