< Maimaitawar Shari’a 14 >
1 Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
Ye are sons of Jehovah your God: ye shall not cut yourselves, nor make any baldness between your eyes for a dead person.
2 gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
For thou art a holy people unto Jehovah thy God, and thee hath Jehovah chosen for a people of possession unto himself, out of all the peoples that are upon the face of the earth.
3 Kada ku ci wani haramtaccen abu.
Thou shalt not eat any abominable thing.
4 Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
These are the beasts which ye shall eat: the ox, the sheep, and the goat;
5 mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
the hart, and the gazelle, and the stag, and the wild goat, and the dishon and the oryx, and the wild sheep.
6 Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
And every beast that hath cloven hoofs, and the feet quite split open into double hoofs, [and] which cheweth the cud, among the beasts, that ye shall eat.
7 Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
Only these ye shall not eat of those that chew the cud, or of those with hoofs cloven and split open: the camel, and the hare, and the rock-badger; for they chew the cud, but have not cloven hoofs — they shall be unclean unto you;
8 Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
and the swine, for it hath cloven hoofs, yet cheweth not the cud — it shall be unclean unto you. Of their flesh shall ye not eat, and their carcase shall ye not touch.
9 Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
These shall ye eat of all that are in the waters: whatsoever hath fins and scales shall ye eat;
10 Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
but whatsoever hath not fins and scales ye shall not eat: it shall be unclean unto you.
11 Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
All clean birds shall ye eat.
12 Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
But these are they of which ye shall not eat: the eagle, and the ossifrage, and the sea-eagle,
13 duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
and the falcon, and the kite, and the black kite after its kind;
and every raven after its kind;
15 jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
and the female ostrich, and the male ostrich, and the sea-gull, and the hawk after its kind;
16 da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
the owl, and the ibis and the swan,
17 kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
and the pelican, and the carrion vulture, and the gannet,
18 zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
and the stork, and the heron after its kind, and the hoopoe, and the bat.
19 Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
And every winged crawling thing shall be unclean unto you; they shall not be eaten.
20 Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
All clean fowls shall ye eat.
21 Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
Ye shall eat of no carcase; thou shalt give it unto the stranger that is within thy gates, that he may eat it, or sell it unto a foreigner; for thou art a holy people to Jehovah thy God. Thou shalt not boil a kid in its mother's milk.
22 Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
Thou shalt truly tithe all the increase of thy seed, the produce of the field, year by year.
23 Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
And thou shalt eat before Jehovah thy God, in the place which he will choose to cause his name to dwell there, the tithe of thy corn, of thy new wine, and of thine oil, and the firstlings of thy herds and of thy flocks; that thou mayest learn to fear Jehovah thy God continually.
24 Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
And if the way be too long for thee, so that thou art not able to carry it, because the place is too far from thee, which Jehovah thy God will choose to set his name there, when Jehovah thy God blesseth thee;
25 to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
then shalt thou give it for money, and bind the money together in thy hand, and go to the place which Jehovah thy God will choose,
26 Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
and thou shalt give the money for whatever thy soul desireth, for oxen, or for sheep, or for wine, or for strong drink, or for whatever thy soul asketh of thee; and thou shalt eat there before Jehovah thy God, and thou shalt rejoice, thou, and thy house.
27 Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
And thou shalt not forsake the Levite that is within thy gates; for he hath no portion nor inheritance with thee.
28 A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
At the end of three years thou shalt bring forth all the tithe of thine increase the same year, and shalt lay it up within thy gates;
29 saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.
and the Levite — for he hath no portion nor inheritance with thee — and the stranger, and the fatherless, and the widow, that are within thy gates, shall come, and shall eat and be satisfied; that Jehovah thy God may bless thee in all the work of thy hand which thou doest.